ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kamfanin Huawei Na Sin Ke Fadada Moriyar Fasahar Sadarwa A Tanzania

by CMG Hausa
3 years ago
Huawei

Sanin kowa ne cewa a zamanin yau, daya daga muhimman fannonin da ke ingiza ci gaban duniya shi ne fannin fasahar sadarwa, wanda karkashinsa, alummun duniya ke cin gajiyar musayar bayanai da sakwanni ta kafofi daban daban, ciki har da na wayar salula da yanar gizo ko intanet. Hakan ne ma ya sa a kasashe masu tasowa da dama, gwamnatoci ke kara azamar samar da manyan ababen more rayuwa a wannan fanni.

A yan shekarun baya bayan nan, kasar Sin na kara samun manyan nasarori a fannonin fasahar sadarwa ko ICT, matakin da ke kara ingiza ci gaban tattalin arziki da zamantakewar alummunta a dukkanin bangarori. Kuma kamfanonin kasar masu ruwa da tsaki suna kara taka rawar gani wajen fitar da fasahohinsu ga kasashen waje, ta yadda daukacin alummun duniya za su kai ga cin gajiya daga hakan.

  • China Ta Musanta Daukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya

Kamfanin Huawei mai gudanar da ayyukan raya fasahohin sadarwa na zamani na kasar Sin, daya ne daga manyan kamfanonin duniya da suka yi fice a wannan fage. Inda ko da a farkon makon nan ma ya sanya hannu kan wata yarjejeniyar fadada turakun samar da hidimar yanar gizo a kasar Tanzania.

ADVERTISEMENT

Bayan kammalarsa, aikin wanda aka yi wa lakabi da NICTBB, zai samar da hidimar yanar gizo ga gundumomin kasar 23 dake kasar ta gabashin Afirka.

Tuni dai kamfanin na Huawei ya tabbatar da shirinsa na yin aiki tare da tsagin Tanzania, wajen ganin an cimma nasarar kafa manyan ababen more rayuwa da za su warware kalubalen da kasar ke fuskanta a fannin sadarwar yanar gizo, matakin da ko shakka babu zai bunkasa fannin fasahar sadarwa a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

A bangaren gwamnatin Tanzania kuwa, manufar wannan aiki na NICTBB shi ne hade dukkanin yankunan kasar da hidimar yanar gizo. Baya ga haka, aikin zai iya taimakawa Tanzania samun damar dunkulewa ta fuskar hidimar fasahar sadarwa da kasashe makwaftanta, kamar Zambia, da Malawi, da Kenya, da Uganda, da Rwanda, da Burundi.

Lura da wannan manufa, muna iya cewa kamfanin Huawei na kasar Sin na taka rawar gani wajen bunkasa fasahar sadarwa a kasashen Afirka, yayin da kasashen nahiyar ke fafutukar samun ci gaba a wannan muhimmin fanni, mai ba da damar bunkasa tattalin arziki da kyautata jin dadin bil adama. (Saminu Hassan)

Huawei
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026
Daga Birnin Sin

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma’a A Matsayin Ranar Sallah

Da Dumi-Dumi: Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma'a A Matsayin Ranar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.