• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Bunkasa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Haskaka Wa Kasashe Masu Tasowa Hanyar Tabbatar Da Dauwamammen Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Yadda Kasar Sin Ke Bunkasa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Haskaka Wa Kasashe Masu Tasowa Hanyar Tabbatar Da Dauwamammen Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba da jimawa ba da rufe gasar wasannin Olympics na Paris, sai kafofin yada labarai na kasar Amurka suka bayyana damuwarsu cewa, “Ya zuwa shekarar 2050, akasarin sassan duniya ba za su iya gudanar da wasannin Olympics ba sabo da tsananin zafi”. A hakika, duniya na ta kara zafi, kuma bil Adama na kara fuskantar matsanancin yanayi irinsu fari, da ambaliya da sauransu. Mai yiwuwa a nan gaba, za a iya gudanar da wasannin Olympics na lokacin zafi ne kawai a kudancin duniyarmu a lokacin da suke dari. 

 

Domin tinkarar matsalar sauyin yanayi, a shekarar 2020 kasar Sin ta sanar da burin da take neman cimmawa, na kaiwa kololuwar fitar da hayakin Carbon mai dumama yanayi kafin shekarar 2030, da kuma daidaita hayakin Carbon da abubuwan da za su zuke shi kafin shekarar 2060. Yanzu shekaru hudu ke nan, kuma ga shi kasar Sin ta cimma nasarorin a zo a gani a wannan fanni, kuma alkaluman da aka fitar sun shaida cewa, fadin dazuzzukan da aka dasa a kasar Sin ya kasance na farko a duniya, kuma kasar ita ce kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa a duniya, karuwar da ta kai kimanin kaso 1/4 na duk duniya cikin shekaru kusan 20 da suka wuce. Baya ga haka, Sin ta kasance daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashin da suke amfani da shi wajen samar da kayayyaki, kuma ta fi saurin raya makamashin da ake iya sabuntawa a duniya, kana yawan makamashi da ake iya sabuntawa da kasar Sin din ke samarwa na kan gaba a duniya, kuma kasar ta kafa cikakken tsarin samar da sabbin makamashi mafi girma a duniya.

  • Ɗan Takarar Shugaban Ƙaramar Hukuma Zai Biya Naira Miliyan 10 A Kano 
  • Sin Na Shirin Amfani Da Fasahohin Dijital Wajen Bunkasa Magungunan Gargajiya Na Kasar

Ban da haka, a gun wani muhimmin taron da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta kira a kwanan baya, jam’iyyar ta sanar da jerin abubuwan da taken neman cimmawa ta fannin kara zurfafa yin gyare-gyare, ciki har da “gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga dukkan fannoni”. A kwanakin baya kuma, kwamitin kolin jam’iyyar da kuma majalisar gudanarwar kasar sun samar da “ra’ayoyi a kan gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga dukkan fannoni”, kuma hakan ya zama karon farko da kasar Sin ta tsara ayyukan da suka shafi gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga matakin kasa.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Duk wadannan abubuwa sun faru ne sakamakon niyyar kasar Sin ta aiwatar da tunanin nan na “kyakkyawan muhalli kadara ce mai kima”. A sakamakon wannan tunani, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi ta kara kyautata, haka kuma ya haskaka wa kasashe masu tasowa hanyar tabbatar da dauwamammen ci gaba.

 

Hasali ma dai, kasar Sin ta riga ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye masu nasaba da samar da makamashi masu tsabta, da kuma tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, kuma yawan lantarki da tashoshin samar da wutar lantarki ta zafin rana da kamfanonin kasar Sin suka gina tare da hadin gwiwar kasashen Afirka suke iya samarwa, tuni ya zarce KW miliyan 1.5, matakin da ya sa kasar ke sahun gaba a duniya wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka ta fannin kiyaye muhalli.

 

Yau rana ce ta kiyaye muhalli ta kasar Sin a karo na biyu. Duniyarmu gida ne na bai daya ga dukkanin dan Adam, kuma makomar dan Adam daya ce a fannin tinkarar matsalolin muhalli. A yayin da kasar Sin ke ci gaba da kokarin inganta muhallin halittu na cikin gida, za ta kuma ci gaba da samar da gudummawa, da hada hannu da sassan kasa da kasa, musamman ma kasashen Afirka, don kara inganta muhallin duniyarmu baki daya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Next Post

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

6 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.