• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Bunkasa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Haskaka Wa Kasashe Masu Tasowa Hanyar Tabbatar Da Dauwamammen Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yadda Kasar Sin Ke Bunkasa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Haskaka Wa Kasashe Masu Tasowa Hanyar Tabbatar Da Dauwamammen Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba da jimawa ba da rufe gasar wasannin Olympics na Paris, sai kafofin yada labarai na kasar Amurka suka bayyana damuwarsu cewa, “Ya zuwa shekarar 2050, akasarin sassan duniya ba za su iya gudanar da wasannin Olympics ba sabo da tsananin zafi”. A hakika, duniya na ta kara zafi, kuma bil Adama na kara fuskantar matsanancin yanayi irinsu fari, da ambaliya da sauransu. Mai yiwuwa a nan gaba, za a iya gudanar da wasannin Olympics na lokacin zafi ne kawai a kudancin duniyarmu a lokacin da suke dari. 

 

Domin tinkarar matsalar sauyin yanayi, a shekarar 2020 kasar Sin ta sanar da burin da take neman cimmawa, na kaiwa kololuwar fitar da hayakin Carbon mai dumama yanayi kafin shekarar 2030, da kuma daidaita hayakin Carbon da abubuwan da za su zuke shi kafin shekarar 2060. Yanzu shekaru hudu ke nan, kuma ga shi kasar Sin ta cimma nasarorin a zo a gani a wannan fanni, kuma alkaluman da aka fitar sun shaida cewa, fadin dazuzzukan da aka dasa a kasar Sin ya kasance na farko a duniya, kuma kasar ita ce kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa a duniya, karuwar da ta kai kimanin kaso 1/4 na duk duniya cikin shekaru kusan 20 da suka wuce. Baya ga haka, Sin ta kasance daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashin da suke amfani da shi wajen samar da kayayyaki, kuma ta fi saurin raya makamashin da ake iya sabuntawa a duniya, kana yawan makamashi da ake iya sabuntawa da kasar Sin din ke samarwa na kan gaba a duniya, kuma kasar ta kafa cikakken tsarin samar da sabbin makamashi mafi girma a duniya.

  • Ɗan Takarar Shugaban Ƙaramar Hukuma Zai Biya Naira Miliyan 10 A Kano 
  • Sin Na Shirin Amfani Da Fasahohin Dijital Wajen Bunkasa Magungunan Gargajiya Na Kasar

Ban da haka, a gun wani muhimmin taron da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta kira a kwanan baya, jam’iyyar ta sanar da jerin abubuwan da taken neman cimmawa ta fannin kara zurfafa yin gyare-gyare, ciki har da “gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga dukkan fannoni”. A kwanakin baya kuma, kwamitin kolin jam’iyyar da kuma majalisar gudanarwar kasar sun samar da “ra’ayoyi a kan gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga dukkan fannoni”, kuma hakan ya zama karon farko da kasar Sin ta tsara ayyukan da suka shafi gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga matakin kasa.

 

Labarai Masu Nasaba

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Duk wadannan abubuwa sun faru ne sakamakon niyyar kasar Sin ta aiwatar da tunanin nan na “kyakkyawan muhalli kadara ce mai kima”. A sakamakon wannan tunani, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi ta kara kyautata, haka kuma ya haskaka wa kasashe masu tasowa hanyar tabbatar da dauwamammen ci gaba.

 

Hasali ma dai, kasar Sin ta riga ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye masu nasaba da samar da makamashi masu tsabta, da kuma tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, kuma yawan lantarki da tashoshin samar da wutar lantarki ta zafin rana da kamfanonin kasar Sin suka gina tare da hadin gwiwar kasashen Afirka suke iya samarwa, tuni ya zarce KW miliyan 1.5, matakin da ya sa kasar ke sahun gaba a duniya wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka ta fannin kiyaye muhalli.

 

Yau rana ce ta kiyaye muhalli ta kasar Sin a karo na biyu. Duniyarmu gida ne na bai daya ga dukkanin dan Adam, kuma makomar dan Adam daya ce a fannin tinkarar matsalolin muhalli. A yayin da kasar Sin ke ci gaba da kokarin inganta muhallin halittu na cikin gida, za ta kuma ci gaba da samar da gudummawa, da hada hannu da sassan kasa da kasa, musamman ma kasashen Afirka, don kara inganta muhallin duniyarmu baki daya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Next Post

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Related

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

2 days ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

5 days ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

2 weeks ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

2 weeks ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

2 weeks ago
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.