ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Bunkasa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Haskaka Wa Kasashe Masu Tasowa Hanyar Tabbatar Da Dauwamammen Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Ba da jimawa ba da rufe gasar wasannin Olympics na Paris, sai kafofin yada labarai na kasar Amurka suka bayyana damuwarsu cewa, “Ya zuwa shekarar 2050, akasarin sassan duniya ba za su iya gudanar da wasannin Olympics ba sabo da tsananin zafi”. A hakika, duniya na ta kara zafi, kuma bil Adama na kara fuskantar matsanancin yanayi irinsu fari, da ambaliya da sauransu. Mai yiwuwa a nan gaba, za a iya gudanar da wasannin Olympics na lokacin zafi ne kawai a kudancin duniyarmu a lokacin da suke dari. 

 

Domin tinkarar matsalar sauyin yanayi, a shekarar 2020 kasar Sin ta sanar da burin da take neman cimmawa, na kaiwa kololuwar fitar da hayakin Carbon mai dumama yanayi kafin shekarar 2030, da kuma daidaita hayakin Carbon da abubuwan da za su zuke shi kafin shekarar 2060. Yanzu shekaru hudu ke nan, kuma ga shi kasar Sin ta cimma nasarorin a zo a gani a wannan fanni, kuma alkaluman da aka fitar sun shaida cewa, fadin dazuzzukan da aka dasa a kasar Sin ya kasance na farko a duniya, kuma kasar ita ce kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa a duniya, karuwar da ta kai kimanin kaso 1/4 na duk duniya cikin shekaru kusan 20 da suka wuce. Baya ga haka, Sin ta kasance daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashin da suke amfani da shi wajen samar da kayayyaki, kuma ta fi saurin raya makamashin da ake iya sabuntawa a duniya, kana yawan makamashi da ake iya sabuntawa da kasar Sin din ke samarwa na kan gaba a duniya, kuma kasar ta kafa cikakken tsarin samar da sabbin makamashi mafi girma a duniya.

ADVERTISEMENT
  • Ɗan Takarar Shugaban Ƙaramar Hukuma Zai Biya Naira Miliyan 10 A Kano 
  • Sin Na Shirin Amfani Da Fasahohin Dijital Wajen Bunkasa Magungunan Gargajiya Na Kasar

Ban da haka, a gun wani muhimmin taron da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta kira a kwanan baya, jam’iyyar ta sanar da jerin abubuwan da taken neman cimmawa ta fannin kara zurfafa yin gyare-gyare, ciki har da “gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga dukkan fannoni”. A kwanakin baya kuma, kwamitin kolin jam’iyyar da kuma majalisar gudanarwar kasar sun samar da “ra’ayoyi a kan gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga dukkan fannoni”, kuma hakan ya zama karon farko da kasar Sin ta tsara ayyukan da suka shafi gaggauta sauya salon bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma ta yadda zai zama mai kiyaye muhalli daga matakin kasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Duk wadannan abubuwa sun faru ne sakamakon niyyar kasar Sin ta aiwatar da tunanin nan na “kyakkyawan muhalli kadara ce mai kima”. A sakamakon wannan tunani, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi ta kara kyautata, haka kuma ya haskaka wa kasashe masu tasowa hanyar tabbatar da dauwamammen ci gaba.

 

Hasali ma dai, kasar Sin ta riga ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye masu nasaba da samar da makamashi masu tsabta, da kuma tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, kuma yawan lantarki da tashoshin samar da wutar lantarki ta zafin rana da kamfanonin kasar Sin suka gina tare da hadin gwiwar kasashen Afirka suke iya samarwa, tuni ya zarce KW miliyan 1.5, matakin da ya sa kasar ke sahun gaba a duniya wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka ta fannin kiyaye muhalli.

 

Yau rana ce ta kiyaye muhalli ta kasar Sin a karo na biyu. Duniyarmu gida ne na bai daya ga dukkanin dan Adam, kuma makomar dan Adam daya ce a fannin tinkarar matsalolin muhalli. A yayin da kasar Sin ke ci gaba da kokarin inganta muhallin halittu na cikin gida, za ta kuma ci gaba da samar da gudummawa, da hada hannu da sassan kasa da kasa, musamman ma kasashen Afirka, don kara inganta muhallin duniyarmu baki daya.

 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.