• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kwallon Kafa Ke Karfafa Cimma Burin ’Yan Mata Da Ke Karatu A Jihar Xinjiang

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Kasar Sin
0
Xinjiang
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gulikiz Igarbeydi mai horas da wasan kwallon kafa ce a jihar Xinjiang dake arewa maso yammacin kasar Sin. Yayin da take matashiya ’yar makaranta, ta kan tambayi kan ta cewa, yaushe ne ’yan mata za su samu damar buga kwallon kafa kamar takwarori su maza a Xinjiang?

Lokacin da take karatu a kwaleji, Gulikiz ta yi kokarin samun ’yan uwan ta ’yan mata masu sha’awar buga kwallo, amma hakan na da wuya, don haka ta kan jira ne kawai idan yara maza sun dakata sannan ta dan buga kwallo.
A yanzu Gulikiz na da shekaru 46 da haihuwa, kuma ko shakka babu abubuwa sun sauya sosai. Gulikiz ta riga ta zama kocin kwallon kafa ajin ’yan mata, a wata makarantar midil dake garin Bageqi a gundumar Hetian. Tana horas da tawagar ’yan mata 27, kuma akwai karin wasu dake sonsu ma su shiga kungiyar da take horaswa.

  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Game da sauyin da take gani a yanzu, Gulikiz ta ce “Lokacin da nake dalibta, iyaye na kan ce wasan kwallon kafa na maza ne, kuma malamai ma na cewa kwallon kafa na bukatar takara mai tsanani, don haka wasan bai dace da mata ba. A wannan lokaci cikin shekarun 1990 a jihar Xinjiang, akwai wannan yanayi da aka nuna bambanci tsakanin maza da mata.

A ajin da ta yi karatu, Gulikiz ta ce dalibai su 77 ne, kuma su 7 ne kacal mata. Kana in ban da ita, ba wata mace dake buga kwallon kafa.

Xinjiang
•yadda ake gudanar da gasar wasan kwallon kafa mata a tsakanin makarantun jihar Xinjiang

Ta kara da cewa, “A wancan lokaci mutane na yiwa mace dake buga kwallon kafa wani irin kallo, har ma makwafta kan nuna ta da yatsa”. Amma bisa sha’awar ta ga kwallon kafa, Gulikiz ta zama mai koyar da wasannin motsa jiki a makarantar midil dake Hetian, bayan da ta kammala karatu daga makaranta, duk da hakan ba abu ne da ta cimma cikin sauki ba.

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

Ta ce “A da can, iyaye da dama ba su damu da ilimin yaran su ba, abu ne mai sauki yaro ya ki zuwa makaranta. Kuma ’yan mata na jin kunyar yin wasannin motsa jiki tare da takwarorinsu maza, kuma ba su cika son motsa jiki sosai ba.”

Amma a shekarun baya bayan nan, Gulikiz na ganin al’ummun Xinjiang sun samu karin damammaki na yin tafiye-tafiye zuwa wurare masu yawa. Kaza lika, ta hanyar kallon talabijin da shiga yanar gizo, suna kara fahimtar inda duniya ta sa gaba, tunaninsu ya kara fadada, wanda hakan ke sauya musu alkibla game da yadda za su yi renon yaran su ta fuskar ba su ilimi, da ma batun shigar yara mata cikin wasannin kwallon kafa.

Xinjiang
•Yadda dalibai mata suke wasan kwallon kafa

A shekarun baya bayan nan, sha’anin kwallon kafa a Xinjiang ya samu bunkasa, bisa tallafin da lardunan kasar Sin da dama ke bayarwa. Yanzu haka larduna 19 da birane, ciki har da Beijing, da Shanghai, da Jiangsu, suna hadin gwiwar baiwa biranen dake Xinjiang tallafi a fannonin raya wasan. Tun daga shekarar 2020 zuwa yanzu, tallafin na su ya kai sama da kudin Sin yuan biliyan 10, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.37. Kari kan hakan, malaman makarantu sama da 14,000 sun samu horon kyautata koyar da dalibai a Xinjiang, inda da daman su suke taimakawa wajen raya sha’anin kwallon kafa a jihar.

Gulikiz ta ce “Ina jin dai mafarki na ya zama gaskiya cikin ‘yan shekaru kadan.”
Da take bayyana yanayin da ake ciki, shugabar makarantar midil ta garin Bageqi Bai Huilin, ta ce “Kusan dukkanin makarantu dake gundumar Hetian dake kudancin jihar Xinjiang sun riga sun kafa kungiyoyin kwallon kafa na mata. Kuma adadin ’yan mata dake shiga wasan na kwallon kafa ya kai kaso kusan 20 bisa dari, bisa jimillar ’yan matan makarantun.”

Alkaluma sun nuna cewa, makarantu 799 sun shiga gasar lashe kofin kwallon kafa ta mata mai lakabin “Hemei Cup”, gasar da gundumar Hetian ta shirya a farkon watanni shida na shekarar nan ta 2023. Kaza lika a gundumar Kizilsu Kirgiz, an gudanar da gasanni sama da 20 cikin shekarar nan ta bana, gasannin da suka samu halartar ’yan makaranta kusan 13,000 daga firamare, da midil, ciki har da ’yan mata da adadin su ya kai rabin jimillar ’yan wasan. Ga wadannan yara mata, karfin gwiwar su shi ne babban jarin su, wanda kuma suke samu daga taka leda yadda ya kamata.

Xinjiang
•Yadda kungiyar wasan kwallon kafa mata din ta yi horaswa

Munire Adili, daliba ce dake aji na 5 a makarantar firamare dake garin Gujiangbage na birnin Hetian, ta kuma ce “Yayin da mahaifiyata ta ga shaidar nasarar da na samu a gasar kwallon kafa, ta yi matukar farin ciki, har ta nunawa makwaftan mu wannan takardar shaida.”

Kusan rabin shekarar nan, Munire ta rika sha’awar wasan kwallon kafa a duk lokacin da take kallo mata suna taka leda a makaranta. Da taimakon mahaifiyarta, ta shiga gwaji, tare da yin nasara mai yawa kafin ta samu zama mai tsaron gida, a kungiyar kwallon kafar su. Ga matashiya Munire, lashe wasanni na kara mata kwarin gwiwar haye wahalhalun rauni da take samu yayin da take atisaye.

A cewar ta “Idan kwallo ta daki mutum a fuska ko a jikinta, ana jin ciwo sosai, amma kocinmu tana karfafa mana gwiwa da cewa, kwallo ba ta da baki balle ta yi cizo. Ina fatan ci gaba da yin atisaye sosai domin samun damar wakiltar makarantar mu a gasanni daban daban a nan gaba, ta yadda zan samu zarafin ganin sauran sassan duniya.”

Ita ma daliba Bumairemu Ali, wadda ke aji na 9 a makarantar midil dake garin Bageqi, ta samu damar ziyartar wurare daban daban a jihar Xinjiang sanadiyyar kwallon kafa.
Ta kuma ce “Na yi wasu kawaye daga sassan kabilu daban daban ta hanyar buga wasan kwallo a wurare masu yawa. Mu kan yi musayar fahimta ta yanar gizo, game da kwallo da harkokin karatu.”

Xinjiang
•Kungiyar wasan kwallon kafa mata ta makarantar midil dake garin Bageqi

Makarantar garin Bageqi, na amfani da kudaden da take samu wajen taimakawa daliban ta ’ya’yan makiyaya da dukkanin abubuwan da suke bukata na buga wasa, kama daga takalma, da sufuri, da matsuguni, ta yadda za su samu damar shiga a dama da su a gasannin da ake shiryawa.

Yanzu haka, Bumairemu ta kusa kammala karatun midil, tana kuma da kyakkyawan fata game da makomar rayuwarta. Game da hakan, ta ce “Ina da zabi mai yawa a nan gaba, amma kwallon kafa na kan gaba cikin abubuwan da zan baiwa muhimmanci.”

A duk lokacin da koci Gulikiz ta sanya matasan dalibai mata da take horaswa a gaba suna taka leda, ta kan samu kwanciyar hankali. Ta tabbatar cewa, a yanzu lokaci ya wuce da iyayen yara mata za su rika kiran su domin su tafi aikin gona, a lokacin da ya kamata a ce suna aji, ko kuma a rika tsokanar su saboda kawai suna buga kwallon kafa.

Kungiyar wasan kwallon kafan mata ta kasar Sin ta taba kasancewa a kan gaba a duniya, amma a shekarun baya baya nan, sakamakon kungiyar na rashin samun nasarori a wasan, ya sa karfin kungiyar bai kai matsayin na gaba a duniya ba, dalilin da ya sa hakan shi ne rashin samun matasa da yara mata masu yawa da suka kware a wasan.

A wadannan shekaru, an kara maida hankali ga wasan kwallon kafa, kasar Sin ta kara nuna goyon baya ga wasan kwallon kafa, inda aka kyautata tsarin raya wasan a makarantun kasar, wannan mataki ya taimaka wajen raya sha’anin wasan kwallon kafa na kasar Sin. A matsayin tushen raya wasan kwallon kafa mata da ma muhimmin bangare na raya wannan sha’ani, aikin raya wasan kwallon kafa mata a makarantu midil da firamare na kasar Sin ya kara jawo hankalin zamantakewar al’ummar kasar.

Tun daga shekarar 2009, gwamnatin jihar Xinjiang ta fara gudanar da ayyukan raya wasan kwallon kafa a makarantun jihar. Jihar Xinjiang tana da fadi, da kabilu da dama, kana jihar Xinjiang jiha ce dake da ’yan kabilar Uygur. Daliban makaranta za su ji dadin wasan da kyautata rayuwarsu ta hanyar buga wasan kwallon kafa. A matsayin wasan dake bukatar mutane da dama, wasan kwallon kafa zai taimakawa dalibai yin hadin gwiwa da juna, da sauike nauyin dake wuyansu, da yin hakuri da sauransu.

Yawancin daliban da ke shiga tawagar mata ta kungiyar kwallon kafa ta matasa ta jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta, daliban kananan kabilu ne, kuma iyali da addini suna shafar wadannan dalibai shiga harkar kwallon kafa. Don haka shiga wasan kwallon kafa zai taimakawa dalibai mata su kara shiga tsarin zamantakewar al’umma da jin dadin zaman rayuwa na zamani. (Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hong KongKasar SinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Next Post

Yadda Karancin Takardun Naira Ke Kara Matsin Rayuwa Ga Talaka

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

3 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

10 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

10 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

11 months ago
Zambiya
Daga Kasar Sin

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

1 year ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Next Post
Takardun Naira

Yadda Karancin Takardun Naira Ke Kara Matsin Rayuwa Ga Talaka

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.