• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Likitoci Sinawa Ke Tallafawa Masu Larurar Ido A Ghana

by CMG Hausa
3 years ago
likitoci

Kamar yadda Bahaushe kan ce “Lafiya Uwar Jiki”, babu mai fushi da ke, mun sani cewa daya daga muhimman fannonin kare lafiyar dan adam shi ne fannin lafiyar ido. Ga wadanda suke fuskantar larurar gani ko ciwon ido, su kan shiga wani yanayi mawuyaci, tare da fafutukar neman magani.

To sai dai a kasar Ghana dake yammacin nahiyar Afirka, masu irin wannan larura sun yi gam-da-katar, domin kuwa, tun daga watan Nuwambar bara, wata tawagar likitocin kasar Sin da aka aike kasar, tana gudanar da tiyata kyauta, ga masu fama da matsalolin ido, ciki har da masu fama da cutar yanar ido ko “cataracts” a Turance.

  • An Saurari Bayani Game Da Yanayin Yaki Da Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

Al’ummun kasar Ghana da dama, sun ci gajiya daga hidimomin kula da idanu da tawagar likitocin na kasar Sin ke bayarwa. Tun daga wancan lokaci zuwa yanzu. Jama’a na samun damar a duba idanunsu, tare da ba su magani, ko ma yi musu aiki idan ta kama, a cibiyar da likitocin na Sin ke aiki, wadda take asabitin ido na LEKMA, a birin Accra, fadar mulkin kasar.

Ga masu karamin karfi dake fama da yanar ido, abu ne mai wahala su iya samun magani, duba da cewa, aikin wannan cuta na da tsada, don haka wasu daga cikinsu, su kan hakura da yanayin da suke ciki, har ta kai ga sun rasa ganin su baki daya. Amma zuwan wannan tawaga ta likitocin ido daga kasar Sin, ya farfado da fatansu na samun lafiya, matakin da ke matukar samun yabo daga dukkanin al’ummar kasar baki daya.

Idan za mu iya tunawa, tun a baya, mahukuntan kasar Sin sun sha alkawarta tallafawa kasashe masu tasowa ta fannin kiwon lafiya, kuma karkashin manufofin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, Sin ta aiwatar da matakai daban daban, na agazawa kasashen Afirka da kayan aiki, da tallafin kwararru, wanda tuni kasashen nahiyar da dama suka ci gajiyar hakan. La’akari da haka, ma iya cewa, Sin tana cika alkawura da ta dauka ga kawayenta na Afirka, kuma kwalliya na biyan kudin sabulu, game yaukakar alakar Sin da abokanta na nahiyar Afirka, da ma burin kasar ta Sin, na samar da al’ummar duniya mai makomar bai daya daga dukkanin fannoni. (Saminu Hassan)

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.