• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Likitoci Sinawa Ke Tallafawa Masu Larurar Ido A Ghana

by CMG Hausa
3 years ago
likitoci

Kamar yadda Bahaushe kan ce “Lafiya Uwar Jiki”, babu mai fushi da ke, mun sani cewa daya daga muhimman fannonin kare lafiyar dan adam shi ne fannin lafiyar ido. Ga wadanda suke fuskantar larurar gani ko ciwon ido, su kan shiga wani yanayi mawuyaci, tare da fafutukar neman magani.

To sai dai a kasar Ghana dake yammacin nahiyar Afirka, masu irin wannan larura sun yi gam-da-katar, domin kuwa, tun daga watan Nuwambar bara, wata tawagar likitocin kasar Sin da aka aike kasar, tana gudanar da tiyata kyauta, ga masu fama da matsalolin ido, ciki har da masu fama da cutar yanar ido ko “cataracts” a Turance.

  • An Saurari Bayani Game Da Yanayin Yaki Da Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

Al’ummun kasar Ghana da dama, sun ci gajiya daga hidimomin kula da idanu da tawagar likitocin na kasar Sin ke bayarwa. Tun daga wancan lokaci zuwa yanzu. Jama’a na samun damar a duba idanunsu, tare da ba su magani, ko ma yi musu aiki idan ta kama, a cibiyar da likitocin na Sin ke aiki, wadda take asabitin ido na LEKMA, a birin Accra, fadar mulkin kasar.

Ga masu karamin karfi dake fama da yanar ido, abu ne mai wahala su iya samun magani, duba da cewa, aikin wannan cuta na da tsada, don haka wasu daga cikinsu, su kan hakura da yanayin da suke ciki, har ta kai ga sun rasa ganin su baki daya. Amma zuwan wannan tawaga ta likitocin ido daga kasar Sin, ya farfado da fatansu na samun lafiya, matakin da ke matukar samun yabo daga dukkanin al’ummar kasar baki daya.

Idan za mu iya tunawa, tun a baya, mahukuntan kasar Sin sun sha alkawarta tallafawa kasashe masu tasowa ta fannin kiwon lafiya, kuma karkashin manufofin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, Sin ta aiwatar da matakai daban daban, na agazawa kasashen Afirka da kayan aiki, da tallafin kwararru, wanda tuni kasashen nahiyar da dama suka ci gajiyar hakan. La’akari da haka, ma iya cewa, Sin tana cika alkawura da ta dauka ga kawayenta na Afirka, kuma kwalliya na biyan kudin sabulu, game yaukakar alakar Sin da abokanta na nahiyar Afirka, da ma burin kasar ta Sin, na samar da al’ummar duniya mai makomar bai daya daga dukkanin fannoni. (Saminu Hassan)

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.