• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ma’aikatan MDD A Nijeriya Suka Girmama Takwarorinsa Da Aka Kashe A Gaza

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Ma’aikatan MDD A Nijeriya Suka Girmama Takwarorinsa Da Aka Kashe A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya (MDD), sun bi sahun takwarorinsu na duniya wajen yin shiru na minti daya domin tunawa da ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya da suka rasa rayukansu a yakin da Isra’ila da Hamas ke ci gaba da yi a Gaza.

Da yake jawabi, mukaddashin babban jami’in MDD a Nijeriya, babban wakilin sashen ci gaban kasashe na UNDP, Mohammed Yahya, ya bayyana cewa, “cikin alhini muke bin sahun dukkan ma’aikatan MDD a fadin duniya wajen yin shiru na minti daya a yau Litinin 13 ga Nuwambar 2023 domin karrama abokan aikinmu da aka kashe a Gaza”.

Ya bayyana haka ne a wani takaitaccen taron da aka yi tare da sassauta tutar Majalisar a babban ofishinta da ke Abuja

  • Hukuncin Zaben Gwamnan Kano: ‘Yansanda Sun Gargadi ‘Yan Siyasa Kan Yunkurin Tayar Da Hargitsi

“Kamar yadda kuke gani, an sassauta tutar Majalisar Dinkin Duniya zuwa rabin turke a matsayin alamar girmamawa a wannan taro. “Ina neman dukkanmu mu yi shiru na tsawon minti daya yayin da muke girmama abokan aikinmu da suka mutu,” in ji shi.

Bugu da kari, ya bukaci dukkan ma’aikatan su nuna alhininsu ga marigayan, yana mai jaddada muhimmancin girmamawa da kuma tunawa da wadanda suka sadaukar da kansu wajen yi wa al’umma ayyukan jin kai hidima.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Domin cika umarnin da aka bayar, har ila yau an yi shiru na minti daya a tsakanin ma’aikata 86 da ke halartar taron koli na Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya da ke gudana a Jihar Neja. Daidai misalin karfe 1:30 na rana, mahalarta taron sun mike tsaye don yin shiru na minti daya domin girmama abokan aikinsu da suka mutu a Gaza.

Bayan shirun na minti dayan ne, Yahaya ya kammala sakon nasa da kyakkyawar ta’aziyya da addu’a, yana mai cewar, “Allah ya sa sun huta.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlhiniGazajimamiMajalisar Dinkin DuniyaMutuwaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Hada Hannu Domin Kyautata Dangantakarsu

Next Post

Muna Fuskantar Manyan Matsaloli – Shettima

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

15 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Cikin Wata 6 Kacal Tinubu Zai Fatattaki Matsalar Tsaro – Shettima

Muna Fuskantar Manyan Matsaloli - Shettima

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.