• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Makafi 44 Suka Zana Jarrabawar JAMB A Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Makafi 44 Suka Zana Jarrabawar JAMB A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu lalurar makanta 44 ne suka zana jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandire (JAMB) ta shekarar 2024 a ranar Litinin a cibiyar musamman da aka ware domin jarrabawar ga makafi a Bauchi da ya gudana a cikin jami’ar ATBU da ke Yelwa. 

Dalibai makafi 44 sun fito ne daga jihohi hudu na arewa maso gabas da suka kunshi Bauchi, Gombe, Yobe da Borno.

  • Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya
  • Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

JAMB a karkashin shirinta na musamman na bai wa masu bukata ta musamman cikakken dama irin ta kowa domin cimma burukansu na rayuwa ne aka zana jarabawar wacce ake yi a cibiyoyi sama da goma a fadin Nijeriya.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan jarabawar, Ko’odinetan jarabawar makafi a Bauchi, Farfesa Salisu Shehu, ya bukaci gwamnatin jihar Bauchi da sauran jihohin da suke arewa maso gabas da su dukufa wajen wayar da kan mutanen da ke fama da lalura ta musamman domin ganin sun samu cin gajiyar shirye-shiryen da JAMB ke yi musu.

A cewarsa, muddin aka wayar da kan masu bukata ta musamman tare da iyayensu tabbas za a samu karin masu shigowa a dama da su wajen zana jarabawar JAMB domin kyautata musu rayuwarsu ta gobe.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

JAMB

Ya nuna gamsuwarsa kan yadda daliban suka nuna da’a a yayin jarabawar, ya ce, an shirya musu komai tun daga zuwansu daga jihohinsu da masaukinsu da abinci da zirga-zirgansu hadi da kudin motan zuwa da komawa dukka kyauta ne.

Shi ma a jawabinsa, kwamishinan yada labarai na jihar Bauchi, Kwamared Usman Dan Turaki, ya nuna farin cikinsa kan kyakkyawar tsarin da JAMB ta yi wajen shigo da masu bukata ta musamman cikin tsarin jarabawar sharar fagen shiga manyan makarantu.

Ya ce, tabbas wannan shirin abun yaba ne domin kowa zai samu damar cimma burinsa, ya na mai cewa ta hanyar masu ta musamman ana iya samun gagarumin cigaba a kasa baki daya.

Ya gode wa gwamnatin tarayya a karkashin Bola Ahmed Tinubu kan yadda take tunawa da kowa a cikin shirye-shiryenta.

Kazalika, ya ce daga cikin muhimman abubuwa da gwamnatin jihar Bauchi a bisa jagoranci Bala Muhammad ta sanya a gaba har da kyautata rayuwar masu bukata ta musamman da kuma sanya su a gaba-gaba wajen kowace irin shirye-shiryen cin gajiyar romon demukuradiyya.

JAMB

Har ila yau mamba a sashin bayar da dama ga kowa ta JAMB, Farfesa Hadiza Isah Bazza ta bukaci daliban da su jajirce wajen ganin sun cimma burukansu na rayuwa musamman a bangaren ilimi.

Ta kuma bukaci iyaye da su cigaba da mara wa ‘ya’yansu da ke fama da bukata ta musamman baya a dukkanin abubuwan da suka sanya a gaba domin su ma suke kai rayuwarsu gaba kamar yadda kowa ke samun dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JambJami'o'in NijeriyaMakafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Sin Dake Amurka: Ana Fatan Amurka Da Sin Su Bi Hanya Daya Don Binciken Yadda Kulla Abota Tsakaninsu

Next Post

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Related

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

15 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 day ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Next Post
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.