• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Makafi 44 Suka Zana Jarrabawar JAMB A Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Makafi 44 Suka Zana Jarrabawar JAMB A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu lalurar makanta 44 ne suka zana jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandire (JAMB) ta shekarar 2024 a ranar Litinin a cibiyar musamman da aka ware domin jarrabawar ga makafi a Bauchi da ya gudana a cikin jami’ar ATBU da ke Yelwa. 

Dalibai makafi 44 sun fito ne daga jihohi hudu na arewa maso gabas da suka kunshi Bauchi, Gombe, Yobe da Borno.

  • Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya
  • Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

JAMB a karkashin shirinta na musamman na bai wa masu bukata ta musamman cikakken dama irin ta kowa domin cimma burukansu na rayuwa ne aka zana jarabawar wacce ake yi a cibiyoyi sama da goma a fadin Nijeriya.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan jarabawar, Ko’odinetan jarabawar makafi a Bauchi, Farfesa Salisu Shehu, ya bukaci gwamnatin jihar Bauchi da sauran jihohin da suke arewa maso gabas da su dukufa wajen wayar da kan mutanen da ke fama da lalura ta musamman domin ganin sun samu cin gajiyar shirye-shiryen da JAMB ke yi musu.

A cewarsa, muddin aka wayar da kan masu bukata ta musamman tare da iyayensu tabbas za a samu karin masu shigowa a dama da su wajen zana jarabawar JAMB domin kyautata musu rayuwarsu ta gobe.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

JAMB

Ya nuna gamsuwarsa kan yadda daliban suka nuna da’a a yayin jarabawar, ya ce, an shirya musu komai tun daga zuwansu daga jihohinsu da masaukinsu da abinci da zirga-zirgansu hadi da kudin motan zuwa da komawa dukka kyauta ne.

Shi ma a jawabinsa, kwamishinan yada labarai na jihar Bauchi, Kwamared Usman Dan Turaki, ya nuna farin cikinsa kan kyakkyawar tsarin da JAMB ta yi wajen shigo da masu bukata ta musamman cikin tsarin jarabawar sharar fagen shiga manyan makarantu.

Ya ce, tabbas wannan shirin abun yaba ne domin kowa zai samu damar cimma burinsa, ya na mai cewa ta hanyar masu ta musamman ana iya samun gagarumin cigaba a kasa baki daya.

Ya gode wa gwamnatin tarayya a karkashin Bola Ahmed Tinubu kan yadda take tunawa da kowa a cikin shirye-shiryenta.

Kazalika, ya ce daga cikin muhimman abubuwa da gwamnatin jihar Bauchi a bisa jagoranci Bala Muhammad ta sanya a gaba har da kyautata rayuwar masu bukata ta musamman da kuma sanya su a gaba-gaba wajen kowace irin shirye-shiryen cin gajiyar romon demukuradiyya.

JAMB

Har ila yau mamba a sashin bayar da dama ga kowa ta JAMB, Farfesa Hadiza Isah Bazza ta bukaci daliban da su jajirce wajen ganin sun cimma burukansu na rayuwa musamman a bangaren ilimi.

Ta kuma bukaci iyaye da su cigaba da mara wa ‘ya’yansu da ke fama da bukata ta musamman baya a dukkanin abubuwan da suka sanya a gaba domin su ma suke kai rayuwarsu gaba kamar yadda kowa ke samun dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JambJami'o'in NijeriyaMakafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Sin Dake Amurka: Ana Fatan Amurka Da Sin Su Bi Hanya Daya Don Binciken Yadda Kulla Abota Tsakaninsu

Next Post

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

2 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

3 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

13 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

14 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 day ago
Next Post
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
JAMB

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.