ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

by Sadiq
2 years ago
Kano

Wani mahaifi mai shekaru 60 mai suna Malam Danjuma da ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35 da kuma Aminu Gaye mai shekaru 35 sun rasa rayukansu yayin ciro wata waya da ta fada masai a kauyen ‘Yar Gwanda da ke karamar hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.

Rahotanni sun bayyana cewar mutanen uku sun makale ne a cikin ramin wata masai yayin da suke kokarin dauko wayar da ta fada ciki a ranar Lahadi.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara
  • Tsaro: Nijeriya Za Ta Karbo Jiragen Yaki 24 Daga Kasar Italiya

Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Abdullahi, ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Ya ce an ceto Alasan da ransa, yayin da sauran ukun kuma aka ceto su a sume amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsu a wani asibiti da ke Bichi.

A cewar Abdullahi, a ranar Lahadi 21 ga watan Afrilu, 2024, hukumar ta samu kiran agaji da misalin karfe 11:00 na safe daga wani Aminu Yar Gwanda, wanda ya sanar da faruwar lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ya ce a lokacin da suka isa wajen, sun tarar da wani Malam Danjuma, mai shekaru 60 ya shiga cikin ramin domin ya ciro wayarsa da ta fada ciki amma ya kasa fitowa.

Ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35, shi ma ya shiga ramin da nufin ceto mahaifinsa amma dukkaninsu suka makale.

Abdullahi, ya kara da cewa mutum na uku, Aminu T Gaye mai shekaru 35, wanda ya yi kokarin ceto su amma ya kasa, kazalika mutum na hudu Abbas Alasan mai shekaru 28 shi ma ya kasa ceto su.

Amma ya ce mutane uku da aka ceto an mika su ga jami’in ‘yansanda na shiyyar Tsanyawa.

Jami’in dan sandan da ya garzaya da su asibiti a Bichi, SP Iro Lado, ya tabbatar da mutuwar mutanen ukun, amma ya ce mutum na hudun na raye.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya

Yanzu-Yanzu: Jami'an Tsaro Sun Cafke Jami'in Binance A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.