ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

by Sadiq
2 years ago
Kano

Wani mahaifi mai shekaru 60 mai suna Malam Danjuma da ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35 da kuma Aminu Gaye mai shekaru 35 sun rasa rayukansu yayin ciro wata waya da ta fada masai a kauyen ‘Yar Gwanda da ke karamar hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.

Rahotanni sun bayyana cewar mutanen uku sun makale ne a cikin ramin wata masai yayin da suke kokarin dauko wayar da ta fada ciki a ranar Lahadi.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara
  • Tsaro: Nijeriya Za Ta Karbo Jiragen Yaki 24 Daga Kasar Italiya

Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Abdullahi, ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Ya ce an ceto Alasan da ransa, yayin da sauran ukun kuma aka ceto su a sume amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsu a wani asibiti da ke Bichi.

A cewar Abdullahi, a ranar Lahadi 21 ga watan Afrilu, 2024, hukumar ta samu kiran agaji da misalin karfe 11:00 na safe daga wani Aminu Yar Gwanda, wanda ya sanar da faruwar lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya ce a lokacin da suka isa wajen, sun tarar da wani Malam Danjuma, mai shekaru 60 ya shiga cikin ramin domin ya ciro wayarsa da ta fada ciki amma ya kasa fitowa.

Ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35, shi ma ya shiga ramin da nufin ceto mahaifinsa amma dukkaninsu suka makale.

Abdullahi, ya kara da cewa mutum na uku, Aminu T Gaye mai shekaru 35, wanda ya yi kokarin ceto su amma ya kasa, kazalika mutum na hudu Abbas Alasan mai shekaru 28 shi ma ya kasa ceto su.

Amma ya ce mutane uku da aka ceto an mika su ga jami’in ‘yansanda na shiyyar Tsanyawa.

Jami’in dan sandan da ya garzaya da su asibiti a Bichi, SP Iro Lado, ya tabbatar da mutuwar mutanen ukun, amma ya ce mutum na hudun na raye.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya

Yanzu-Yanzu: Jami'an Tsaro Sun Cafke Jami'in Binance A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.