ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Makafi 44 Suka Zana Jarrabawar JAMB A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
JAMB

Masu lalurar makanta 44 ne suka zana jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandire (JAMB) ta shekarar 2024 a ranar Litinin a cibiyar musamman da aka ware domin jarrabawar ga makafi a Bauchi da ya gudana a cikin jami’ar ATBU da ke Yelwa. 

Dalibai makafi 44 sun fito ne daga jihohi hudu na arewa maso gabas da suka kunshi Bauchi, Gombe, Yobe da Borno.

  • Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya
  • Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

JAMB a karkashin shirinta na musamman na bai wa masu bukata ta musamman cikakken dama irin ta kowa domin cimma burukansu na rayuwa ne aka zana jarabawar wacce ake yi a cibiyoyi sama da goma a fadin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan jarabawar, Ko’odinetan jarabawar makafi a Bauchi, Farfesa Salisu Shehu, ya bukaci gwamnatin jihar Bauchi da sauran jihohin da suke arewa maso gabas da su dukufa wajen wayar da kan mutanen da ke fama da lalura ta musamman domin ganin sun samu cin gajiyar shirye-shiryen da JAMB ke yi musu.

A cewarsa, muddin aka wayar da kan masu bukata ta musamman tare da iyayensu tabbas za a samu karin masu shigowa a dama da su wajen zana jarabawar JAMB domin kyautata musu rayuwarsu ta gobe.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

JAMB

Ya nuna gamsuwarsa kan yadda daliban suka nuna da’a a yayin jarabawar, ya ce, an shirya musu komai tun daga zuwansu daga jihohinsu da masaukinsu da abinci da zirga-zirgansu hadi da kudin motan zuwa da komawa dukka kyauta ne.

Shi ma a jawabinsa, kwamishinan yada labarai na jihar Bauchi, Kwamared Usman Dan Turaki, ya nuna farin cikinsa kan kyakkyawar tsarin da JAMB ta yi wajen shigo da masu bukata ta musamman cikin tsarin jarabawar sharar fagen shiga manyan makarantu.

Ya ce, tabbas wannan shirin abun yaba ne domin kowa zai samu damar cimma burinsa, ya na mai cewa ta hanyar masu ta musamman ana iya samun gagarumin cigaba a kasa baki daya.

Ya gode wa gwamnatin tarayya a karkashin Bola Ahmed Tinubu kan yadda take tunawa da kowa a cikin shirye-shiryenta.

Kazalika, ya ce daga cikin muhimman abubuwa da gwamnatin jihar Bauchi a bisa jagoranci Bala Muhammad ta sanya a gaba har da kyautata rayuwar masu bukata ta musamman da kuma sanya su a gaba-gaba wajen kowace irin shirye-shiryen cin gajiyar romon demukuradiyya.

JAMB

Har ila yau mamba a sashin bayar da dama ga kowa ta JAMB, Farfesa Hadiza Isah Bazza ta bukaci daliban da su jajirce wajen ganin sun cimma burukansu na rayuwa musamman a bangaren ilimi.

Ta kuma bukaci iyaye da su cigaba da mara wa ‘ya’yansu da ke fama da bukata ta musamman baya a dukkanin abubuwan da suka sanya a gaba domin su ma suke kai rayuwarsu gaba kamar yadda kowa ke samun dama.

JAMB
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.