ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Makafi 44 Suka Zana Jarrabawar JAMB A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
JAMB

Masu lalurar makanta 44 ne suka zana jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandire (JAMB) ta shekarar 2024 a ranar Litinin a cibiyar musamman da aka ware domin jarrabawar ga makafi a Bauchi da ya gudana a cikin jami’ar ATBU da ke Yelwa. 

Dalibai makafi 44 sun fito ne daga jihohi hudu na arewa maso gabas da suka kunshi Bauchi, Gombe, Yobe da Borno.

  • Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya
  • Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

JAMB a karkashin shirinta na musamman na bai wa masu bukata ta musamman cikakken dama irin ta kowa domin cimma burukansu na rayuwa ne aka zana jarabawar wacce ake yi a cibiyoyi sama da goma a fadin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan jarabawar, Ko’odinetan jarabawar makafi a Bauchi, Farfesa Salisu Shehu, ya bukaci gwamnatin jihar Bauchi da sauran jihohin da suke arewa maso gabas da su dukufa wajen wayar da kan mutanen da ke fama da lalura ta musamman domin ganin sun samu cin gajiyar shirye-shiryen da JAMB ke yi musu.

A cewarsa, muddin aka wayar da kan masu bukata ta musamman tare da iyayensu tabbas za a samu karin masu shigowa a dama da su wajen zana jarabawar JAMB domin kyautata musu rayuwarsu ta gobe.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

JAMB

Ya nuna gamsuwarsa kan yadda daliban suka nuna da’a a yayin jarabawar, ya ce, an shirya musu komai tun daga zuwansu daga jihohinsu da masaukinsu da abinci da zirga-zirgansu hadi da kudin motan zuwa da komawa dukka kyauta ne.

Shi ma a jawabinsa, kwamishinan yada labarai na jihar Bauchi, Kwamared Usman Dan Turaki, ya nuna farin cikinsa kan kyakkyawar tsarin da JAMB ta yi wajen shigo da masu bukata ta musamman cikin tsarin jarabawar sharar fagen shiga manyan makarantu.

Ya ce, tabbas wannan shirin abun yaba ne domin kowa zai samu damar cimma burinsa, ya na mai cewa ta hanyar masu ta musamman ana iya samun gagarumin cigaba a kasa baki daya.

Ya gode wa gwamnatin tarayya a karkashin Bola Ahmed Tinubu kan yadda take tunawa da kowa a cikin shirye-shiryenta.

Kazalika, ya ce daga cikin muhimman abubuwa da gwamnatin jihar Bauchi a bisa jagoranci Bala Muhammad ta sanya a gaba har da kyautata rayuwar masu bukata ta musamman da kuma sanya su a gaba-gaba wajen kowace irin shirye-shiryen cin gajiyar romon demukuradiyya.

JAMB

Har ila yau mamba a sashin bayar da dama ga kowa ta JAMB, Farfesa Hadiza Isah Bazza ta bukaci daliban da su jajirce wajen ganin sun cimma burukansu na rayuwa musamman a bangaren ilimi.

Ta kuma bukaci iyaye da su cigaba da mara wa ‘ya’yansu da ke fama da bukata ta musamman baya a dukkanin abubuwan da suka sanya a gaba domin su ma suke kai rayuwarsu gaba kamar yadda kowa ke samun dama.

JAMB
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.