• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

by Primcess Fatima Zarah Mazadu
8 months ago
in Adabi
0
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau ma shafin ADABI na dauke da tattaunawa da wata matashiyar marubuciya, SALMA AHMAD ISAH wadda ta bayyana wa masu karatu yadda ta sha gwagwarmaya wajen fara rubutu. Marubuciyar ta yi bayanai masu yawa game da rubutu har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai tattaunawar tare da FATIMA ZARAH MAZADU (PRINCESS FATIMA) kamar haka:

Da farko masu karatu za su so su ji cikakken sunanki…

Sunana Salma Ahmad Isah.

Ko za ki iya fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

Eh to, da farko dai an haife ni a garin Hadejia, jihar Jigawa. Na yi ‘Primary school’, har zuwa ‘Senior Secondary School’ duka a cikin garin Hadejia, kuma har kawo yanzu ina rayuwa a cikin garin Hadejia.

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma fannin rubuce-rubuce?

A zahirin gaskiya na gano cewa rubutu wata hanya ce wadda zan iya amfani da ita wurin busawa mafarkaina rai, sannan hanya mafi sauki wurin isar da sako zuwa ga al’umma. Wannan shi ne abin da ya ja hankalina a kan rubuce-rubuce.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

Tun ina makaranta nake sha’awar karance-karancen litattafan Hausa, irinsu Jiki Magayi, Komai Nisan Dare, Uwar Gulma da dai makamantansu. A gaskiya wannan shi ne abin da ya fara ba ni sha’awa, sannan na ji cewar ina son ni ma na fara rubutu. To daga haka ne na fara rubuta ‘yan gajerun labarai a bayan litattafaina na makaranta. Kuma tun a wancan lokacin idan na yi na kan ba wa malaminmu na Hausa a makaranta ya duba min. Ganin yadda yake yabawa da kwazon da nake a rubutun ya sa na kara jajircewa ina rubutu ina ajewa, a wasu lokutan kawayena ma kan karba domin su karanta. Tun ina rubuta labarin da bai fi layi biyar ba, har na zo ina cika littafi da rubutu. To daga wannan lokacin ne na daina rubutu a takarda, na fara rubutu a waya. Har Allah ya sa yayata Fatima Ahmad Isah, ta ba ni shawarar tun da na iya rubutun labari kuma ya ba da ma’ana haka, me zai hana na fara rubutu onlayin. To da wannan shawarar ta ta na tsunduma harkar rubutun onlayin, har kawo yau.

Ya farkon farawar ta kasance?

Lokacin da na fara rubutun onlayin na fara da shiga kungiyar marubuta ne, domin koyon ka’idojin rubutun Hausa da Adabi, kuma daga nan ne na fara tasawa har zuwa yau.

Ya batun iyaye lokacin da za ki fara rubutu shin kin fuskanci wani kalubale daga gare su ko kuwa?

A gaskiya na fuskanta, lokacin da ina rubutawa a cikin litattafaina na makaranta idan na zo na ce litattafina ya cika a saya min sabo sai iyaye na su ce ai idan an saya min ma bata shi nake da rubutun wofi. Ko a ce ba za a siya min ‘pen’ ba saboda zan karar da shi a wurin rubutun shirme. Amma daga baya da suka gane cewa rubutun baiwa ce wadda Allah ya azurtani da ita sai suka hakura, domin yanzu komai na yi a kan rubutu sai dai san barka da jinjina.

Kamar wane irin labari kika fi mayar da hankali a kai wajen rubutawa?

Labaran ban tausayi su ne labaran da nake maida hankali wurin rubutawa.

Ko wane tsawon lokaci ne kika kwashe kina rubuta zuwa yanzu?

A kalla yanzu ban wuce shekara daya da fara rubutu ba.

Daga lokacin da ki ka fara zuwa yanzu kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?

Daga lokacin da na fara kawo yanzu na rubuta litattafai guda biyar (5).

Wane labari ne ya zamo bakandamiyarki cikin labaran da ki ka rubuta?

A kaf cikin litattafaina guda biyar na fi son HASKE.

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa kuma me ya sa?

JUYIN KWADO ya fi kowanne bani wahala a cikin litattafaina, dalili kuwa shi ne; labarin ya sha bamban da irin wanda aka saba gani. Labarin JUYIN KWADO labari ne da ya kunshi rayuwa a zamani guda biyu, 11th century da 21st century. Hakan ta sa ya ba ni wahala sosai wurin rubuta shi.

Shin kin taba buga littafi?

A gaskiya har zuwa yanzu ban taba buga littafi ko guda daya ba, ina sa ran buga litattafina na LABARINSU.

Kamar wane irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alal hakika na samu nasarori da dama ta dalilin rubutu, domin ta dalilin wannan rubutun mutane da dama sun sanni, sannan na samu alkairai da dama. Bugu da kari mutane da dama kan min alfarma ta dalilin rubutun.

Ko akwai wani kalubale wanda ki ka taba fuskanta game da rubutu ko daga wajen su kansu marubutan ko kuma makaranta?

Game da rubutu kam babu, haka ma daga wurin makaranta ban taba samu ba, kuma ba na fatan samu ko a nan gaba.

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka game da rubutu wanda ba za ki manta da shi ba?

Akwai wacce ta taba bata min rai game da rubuta, lokacin ina rubuta littafin LABARINSU, kasancewar labari ne a kan illar fyade, kuma fyaden ya afku a kan jarumar labarin, sai wata ta yi min magana kan sam ita ba ta so aka ce an yi wa wance fyade ba. Gaskiya lokacin na ji ba dadi, domin burina shi ne nusar da jama’a illar fyade, amma sai na ga kamar ita ba ta fahimci inda na dosa ba. Dangane da yabo kuwa wannan ba a magana, jama’a da dama na yabawa da rubutun da nake.

Wane abu ne idan ki ka tuna da shi ki ke jin dadi sanadiyyar rubutu?

Idan na tuna da yadda jama’a ke yabon labaran da nake rubutawa kan sa na ji dadi a raina.

Ya ki ka dauki rubutu a wajenki?

Na dauki rubutu a matsayin hanyar busawa mafarkaina rai, sannan hanya mafi sauki don isar da sako.

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Burina shi ne fara ‘scriptwriting’, wannan shi ne babban burina da nake fatan Allah ya cika min shi.

Wace ce gwanarki cikin marubuta?

Khadeeja Candy ita ce gwanata a kodayaushe.

Bayan rubutu kina wata sana’ar ne?

Eh! bayan rubutu ina sana’ar dinki, sannan ina ‘graphic design’.

Ya ki ke iya hada rubutu da dinki da girafik din da ki ke yi?

Eh! to, ko wanne a cikinsu ina ware masa lokacin da zan yi shi, misali na kan ware safiya a matsayin lokacin da zan yi aikina na ‘graphic design’, ko dinki idan ya samu, dare kuma na ware shi a matsayin lokacin da zan yi rubutu.

Wane sako ki ke da shi zuwa ga masoyanki masu karanta labaranki?

Abin da zan ce ga makaranta labarina shi ne, a duk sanda na rubuta labari, bai kamata ku dauka cewa abin da kuke tunani shi ne zai faru ba, domin yadda nake tunani ya bambanta da yadda kuke. Dan haka idan ba zai zamto daya ba, kuma babban burina shi ne ku fuskanci darasin dake cikin labarin, ba wai son ranku ba.

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Ina gaida Khadeeja Candy, my role model, da Zahra Royal Star babbar kawata, tare da Maryam Tijjani Muhammad, da Fatima Ahmad Isah da kuma babbar kawata Maimuna Muhammad.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdabiHausaMalamiRubutu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Comoros Azali Assoumani Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Next Post

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (5)

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

3 weeks ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

4 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

6 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

6 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

6 months ago
Marubuta Na Taimakawa Wajen Bunkasa Rayuwar Al’umma -Miyetti
Adabi

Marubuta Na Taimakawa Wajen Bunkasa Rayuwar Al’umma -Miyetti

8 months ago
Next Post
Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (5)

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (5)

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.