• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
13 hours ago
in Dausayin Musulunci
0
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum wa ramtullahi ta’ala wa barkatuh. Masu karatu idan ba ku manta ba, a makon da ya gabata mun tsaya ne a wurin da Manzon Allah (SAW) ya ce wa Sahabbai duk wanda bai zo da abin hadaya ba ya warware hajjinsa ya mayar da shi umura. Za mu ci gaba.

Sahabbai suka ce “Ya Rasulallahi bai fi kwana hudu a yi Arfa ba”, Annabi (SAW) ya ce “Ku cire haramar kawai, ku yi aski.”

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

“Sai Surakatu Ibn Malik Ibn Ju’ushamu ya mike ya ce “Ya Rasulallahi, wannan hukunci na yanzu (na mayar da Hajji Umura saboda rashin zuwa da abin hadaya), na wannan shekarar ne kawai ko na ko wace shekara ne?”, sai Annabi (SAW) ya shigar da yatsunsa wasu a cikin wasu ya dunkule su ya ce “Umura ta shiga cikin Hajji sau biyu, bari ma dai Umura ta shiga cikin Hajji har abada.” Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya zo daga Yeman da rakuma, yana zuwa ya shiga wurin iyalinsa, ya tarad da matarsa (Sayyida Fadima (AS)) ta yi ado, ya tambaye ta game da hakan alhali ta riga ta yi harama da Hajji? Sai ta ce ma sa: “Babana (SAW) ya ce in yi.” Sayyidina Aliyu ya fada mana a Iraki (in ji Jabir) cewa, “Sai na tafi wurin Babanta don na kai kararta bisa abin da ta aikata kuma in tambaye shi (SAW). Da na fada ma sa, sai Annabi (SAW) ya ce “ta yi gaskiya, ta gaskiya. Kai me ka ce da za ka yi haramar Hajji?” sai na ce, “Cewa na yi; na yi niyyar harama da abin da Annabi ya yi harama da shi.”, daga nan Annabi (SAW) ya ce “Ni ina da abin hadaya, don haka ba zan warware harama ba”. Sayyidina Aliyu ya ce “to nima na zo da rakuma” sai Annabi (SAW) ya ce “to ka shiga cikin hadayata”, sai adadin rakuman da Annabi ya zo da su da wanda Sayyidina Aliyu ya zo da su suka kai yawan guda 100. Daga nan mutanen (da ba su zo da abin hadaya ba) duk suka warware Hajjinsu sai Annabi (SAW) kawai da wadanda suka zo da abin hadayarsu (Sayyidina Aliyu da wani Sahabi guda daya).

“Haka aka zauna har zuwa ranar takwas ga wata, sai Manzon Allah (SAW) ya hau rakumarsa zuwa Mina inda ya yi Sallolin Azahar, La’asar, Magriba, Isha’i, Asubahi duk a can. Da gari ya waye bayan rana ta fito, Annabi (SAW) ya yi umurnin cewa a je a kafa ma sa rumfarsa a Arfa. Annabi (SAW) ya tafi Arfa ya shiga cikin rumfarsa, bai fito ba har sai lokacin da rana ta gota, sai ya bukaci a dora wa rakumarsa sirdi, ya hau aka biyo bayansa zuwa kwarin nan (wurin da Masallacin Namira yake a yanzu) ya yiwa mutane huduba… Bayan ya kammala sai Bilal ya yi wazna aka fara Sallah. Annabi (SAW) ya hada Azuhur da La’asar (Kasaru), daga nan ya hau rakuminsa ya dawo Arfa. Ya kalli Alkibla ya yi ta Zikiransa yana tsaye har zuwa lokacin da rana ta fadi. Sai ya sa Usamatu Ibn Zaidu ya hau bayansa a kan rakuminsa ya kama hanya yana tafiya ba tare da sauri ba yana mai nuni da hannunsa cewa mutane su tafi sannu a hankali, har aka zo Muzdalifa. Annabi (SAW) ya yi mana Magriba da Isha’i da kiran sallah daya, ikama guda biyu amma Isha’i kasru aka yi. Ana kammala sallar sai Annabi (SAW) ya kwanta ba tare da ya yi nafila ko daya ba har zuwa Asalatu. Sannan ya tashi ya yiwa al’umma Sallar Asubahi.

“Daga nan ya hau rakumarsa zuwa Mash’aril Haram (wani Masallaci kafin isa wurin Jifan Shaidan). Ya tsaya a nan yana Kabbarbari har zuwa lokacin da gari ya yi sarari, sannan ya mika hanya inda ya goyo Fadlu Dan Abbas a rakuminsa… Har suka iso Badnil Muhassar (wurin da aka hallaka giwaye) inda ya dan yi sauri har ya shige wurin ya bi ta hanyar da ake isa wurin Jifar Jamratul Akba ya yi Jifa da tsakuwa bakwai. Sannan bayan ya yi addu’a sai ya tafi wurin hadayarsa ya soke rakumi 63 da hannunsa, sai ya mika wa Sayyidina Aliyu mashi ya soke ragowar. Kuma ya yi horo a yanko nama kadan a ko wane rakumi aka dafa ya ci. Daga nan ya yi aski, sai kuma ya hau abin hawansa zuwa Makka ya yi Dawafin saukowa daga Arfa (Dawaful Ifada). Sannan ya yi Safa da Marwa. Bayan ya kammala sai ya je Rijiyar Zamzam, ‘ya’yan Abdulmuddalibi suka bashi guga ya sha.” Wannan shi ne ruwayar Hajjin Annabi (SAW) da Sayyidina Jabiru (RA) ya ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Malamai sun yi bayanin cewa a cikin wannan Hadisin akwai hukunce-hukuncen Aikin Hajji sama da guda 100 a ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Next Post

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Related

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

2 weeks ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

3 weeks ago
Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

1 month ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

2 months ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

2 months ago
Next Post
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.