• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matata Ta Rasu A Kokarin Kare Mutuncinta Daga Masu Garkuwa – Yusuf

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Matata Ta Rasu A Kokarin Kare Mutuncinta Daga Masu Garkuwa – Yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mazaunin garin Jibiya da ke Jihar Katsina, Aminu Yusuf ya ba da labarin yadda matarsa, Malama Ladi, wacce ke shayar da jariri da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da ita, ta zabi ta yi shahada a maimakon bari daya daga cikin masu garkuwa ya tursasa mata aurenshi.

Matar wacce ta rasu a lokacin da dan bindigan ya yi kokarin kwanciyar aure da ita. Ta bi dukkanin matakan da suka dace wajen kin amince masa. Wani abun takaici ma shi ne, masu garkuwan sai da suka karbi kudin fansa da nufin za su saki matar, amma suka aikata mata wannan danyen aikin.

  • Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al’umma
  • Mutum Miliyan 2 Za Su Ci Gajiyar Tallafin Kiwon Lafiya A Bauchi

A wani sautin murya na tattaunawar da ta wakana tsakanin mijinta da daya daga cikin kwamandojin masu garkuwa da mutanen da aka yi ta yadawa a kafafen sadarwar zamani. An ji shugaban masu garkuwan na bayanin yadda daya daga cikin yaransa ya yi da wacce suka kaman, kuma da yadda shi Yusuf din ke rokon su dawo masa da gawar matar tasa.

A hirarsa da LEADERSHIP, Yusuf ya yi karin hasken abubuwan da suka wakana har suka janyo kashe masa mata, ya ce, tun lokacin da abun ya faru hankalinsa a tashe yake ko barci baya iyawa, duk kokarin da suka yi na ceto matar, amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

Lamarin ya faru ne a tsakanin Magama-Jibiya da ke karamar hukumar Jibiya a Jihar Katsina, abun ya tada hankalin jama’a da ba su mamaki matuka ganin yadda mutane ke gwagwarmayar tsira da rayuwarsu kan halin matsatsin tattalin arziki da ake ciki a kasar nan a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Da jaridar LEADERSHIP ta ziyarci gidan Yusuf da ke Magama-Jibiya domin samun labarin rashin imani da zalumcin da ya samu matarsa. Ya ba da labarin yadda suka yi ta tattaunawa da shugaban masu garkuwa da mutanen domin ganin an samu daidaito kan kudin fansa, amma daga baya kuma lamarin ya gagara.

 A cewarsa, shugaban masu garkuwan bayan da aka sace matarsa sun tuntubeshi ta wayar tarho, inda suka bukaci ya biyasu naira miliyan 10 a matsayin kudin fansar matarsa. Ya yi ta rokonsu cewa a rayuwarsa gabaki daya bai taba rike irin wannan kudin masu yawa ba.

Ya ce bayan kwanaki da tattaunawa da su, shugaban masu garkuwan ya rage kudin zuwa naira miliyan biyar, har suka cimma matsaya a kan naira miliyan biyu, amma iyaka abun da suka iya tarawa kawai shi ne naira dubu dari bakwai da wayoyin zamani manya guda uku da suka kai wa ‘yan bindigar.

 “Shugaban masu garkuwan ya shaida min cewa zai yi tafiya zuwa wani wajen, amma na ci gaba da tattaunawa da yaronsa.

 “Nan take na sayar da motata a kan kudi naira dubu dari biyar, sannan ina son na sayar da gidana amma ban samu mutumin da zai saya ba saboda halin matsalolin tattalin arzikin da ake ciki. Na samu damar harhada wasu ‘yan kudi kalilan daga abokai da ‘yan’uwa da makwafta. Gaba daya dai a takaice mun hada naira dubu dari bakwai da wayoyin ‘Andirol’ guda uku.

 “Masu garkuwan sun amince cewa za su hadu da mu, mun kuma tattauna da surukata kan yadda za ta kai musu kudin. Ta amince kuma wannan shi ne hakikanin abun da muka tsara, saboda muna fargabar kar su sake cafke wani idan aka kai kudin.

 “Ta kai musu kudin kuma sun yi alkawarin za su sake ta a washegari, amma abun takaici ba su yi hakan ba. Tun daga wannan lokaci wayarsu ba ta shiga.

 “Bayan wasu ‘yan lokutan, na fara jin jita-jitan cewa ‘yan bindigan sun kashe matata. Sannan wata yarinya da aka yi garkuwa da ita ta tabbatar min da wannan daga baya. Sun kasance tare da matata a inda aka tsare su. A cewarta, matar tawa an tursasa mata yin aure da wani daga cikin masu garkuwan, a lokacin da ya yi kokarin kwanciya da ita, ta ki amincewa ta ba shi hadin kai, ta zabi ta rasa ranta da ta mika kanta da mutuncinta, hakan ya sanya ‘yan bindiga suka harbe ta da harsashi har sau biyu,” in ji shi.

 Yusuf ya ce tun lokacin da suka tabbatar da kisan matar tasa, ya fadi ya suma, kuma a halin yanzu rayuwa ta masa kunci domin kula da ‘ya’ya biyu da suka haifa da matarsa.

“Matata ta rasu ta bar ‘ya’ya biyu, dayansu na farko shekaransa uku a duniya, kaninsa kuma shekaransa daya wanda a halin yanzu yana shan mama.

 “Lokacin da ‘yan bindigan suka yi garkuwa da mamarsa, daya daga cikin yarona ya yi kokarin bin mahaifiyarsa, amma ta jajirce ta ce ka da ya biyo ta.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Hukumar ‘Yan Gudun Hijira, Ya Karbo Wa Zamfara Kayan Tallafi

Next Post

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Related

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

2 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

3 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

3 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

4 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

7 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3
Labarai

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

8 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.