ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matata Ta Rasu A Kokarin Kare Mutuncinta Daga Masu Garkuwa – Yusuf

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Yusuf

Wani mazaunin garin Jibiya da ke Jihar Katsina, Aminu Yusuf ya ba da labarin yadda matarsa, Malama Ladi, wacce ke shayar da jariri da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da ita, ta zabi ta yi shahada a maimakon bari daya daga cikin masu garkuwa ya tursasa mata aurenshi.

Matar wacce ta rasu a lokacin da dan bindigan ya yi kokarin kwanciyar aure da ita. Ta bi dukkanin matakan da suka dace wajen kin amince masa. Wani abun takaici ma shi ne, masu garkuwan sai da suka karbi kudin fansa da nufin za su saki matar, amma suka aikata mata wannan danyen aikin.

  • Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al’umma
  • Mutum Miliyan 2 Za Su Ci Gajiyar Tallafin Kiwon Lafiya A Bauchi

A wani sautin murya na tattaunawar da ta wakana tsakanin mijinta da daya daga cikin kwamandojin masu garkuwa da mutanen da aka yi ta yadawa a kafafen sadarwar zamani. An ji shugaban masu garkuwan na bayanin yadda daya daga cikin yaransa ya yi da wacce suka kaman, kuma da yadda shi Yusuf din ke rokon su dawo masa da gawar matar tasa.

ADVERTISEMENT

A hirarsa da LEADERSHIP, Yusuf ya yi karin hasken abubuwan da suka wakana har suka janyo kashe masa mata, ya ce, tun lokacin da abun ya faru hankalinsa a tashe yake ko barci baya iyawa, duk kokarin da suka yi na ceto matar, amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

Lamarin ya faru ne a tsakanin Magama-Jibiya da ke karamar hukumar Jibiya a Jihar Katsina, abun ya tada hankalin jama’a da ba su mamaki matuka ganin yadda mutane ke gwagwarmayar tsira da rayuwarsu kan halin matsatsin tattalin arziki da ake ciki a kasar nan a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Da jaridar LEADERSHIP ta ziyarci gidan Yusuf da ke Magama-Jibiya domin samun labarin rashin imani da zalumcin da ya samu matarsa. Ya ba da labarin yadda suka yi ta tattaunawa da shugaban masu garkuwa da mutanen domin ganin an samu daidaito kan kudin fansa, amma daga baya kuma lamarin ya gagara.

 A cewarsa, shugaban masu garkuwan bayan da aka sace matarsa sun tuntubeshi ta wayar tarho, inda suka bukaci ya biyasu naira miliyan 10 a matsayin kudin fansar matarsa. Ya yi ta rokonsu cewa a rayuwarsa gabaki daya bai taba rike irin wannan kudin masu yawa ba.

Ya ce bayan kwanaki da tattaunawa da su, shugaban masu garkuwan ya rage kudin zuwa naira miliyan biyar, har suka cimma matsaya a kan naira miliyan biyu, amma iyaka abun da suka iya tarawa kawai shi ne naira dubu dari bakwai da wayoyin zamani manya guda uku da suka kai wa ‘yan bindigar.

 “Shugaban masu garkuwan ya shaida min cewa zai yi tafiya zuwa wani wajen, amma na ci gaba da tattaunawa da yaronsa.

 “Nan take na sayar da motata a kan kudi naira dubu dari biyar, sannan ina son na sayar da gidana amma ban samu mutumin da zai saya ba saboda halin matsalolin tattalin arzikin da ake ciki. Na samu damar harhada wasu ‘yan kudi kalilan daga abokai da ‘yan’uwa da makwafta. Gaba daya dai a takaice mun hada naira dubu dari bakwai da wayoyin ‘Andirol’ guda uku.

 “Masu garkuwan sun amince cewa za su hadu da mu, mun kuma tattauna da surukata kan yadda za ta kai musu kudin. Ta amince kuma wannan shi ne hakikanin abun da muka tsara, saboda muna fargabar kar su sake cafke wani idan aka kai kudin.

 “Ta kai musu kudin kuma sun yi alkawarin za su sake ta a washegari, amma abun takaici ba su yi hakan ba. Tun daga wannan lokaci wayarsu ba ta shiga.

 “Bayan wasu ‘yan lokutan, na fara jin jita-jitan cewa ‘yan bindigan sun kashe matata. Sannan wata yarinya da aka yi garkuwa da ita ta tabbatar min da wannan daga baya. Sun kasance tare da matata a inda aka tsare su. A cewarta, matar tawa an tursasa mata yin aure da wani daga cikin masu garkuwan, a lokacin da ya yi kokarin kwanciya da ita, ta ki amincewa ta ba shi hadin kai, ta zabi ta rasa ranta da ta mika kanta da mutuncinta, hakan ya sanya ‘yan bindiga suka harbe ta da harsashi har sau biyu,” in ji shi.

 Yusuf ya ce tun lokacin da suka tabbatar da kisan matar tasa, ya fadi ya suma, kuma a halin yanzu rayuwa ta masa kunci domin kula da ‘ya’ya biyu da suka haifa da matarsa.

“Matata ta rasu ta bar ‘ya’ya biyu, dayansu na farko shekaransa uku a duniya, kaninsa kuma shekaransa daya wanda a halin yanzu yana shan mama.

 “Lokacin da ‘yan bindigan suka yi garkuwa da mamarsa, daya daga cikin yarona ya yi kokarin bin mahaifiyarsa, amma ta jajirce ta ce ka da ya biyo ta.”

Yusuf
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.