• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ministan Yaɗa Labarai Ya Karɓi Baƙuncin ‘Yan Jaridar Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Ministan Yaɗa Labarai Ya Karɓi Baƙuncin ‘Yan Jaridar Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi maraba da sakin wasu ‘yan jarida biyu da aka sace daga gidajensu da ke bayan garin Kaduna a ƙarshen makon jiya.

Da yake jawabi a lokacin da ya karɓi baƙuncin ‘yan jaridun biyu, wato AbdulGafar Alabelewe na jaridar The Nation da AbdulRaheem Aodu na jaridar Blueprint, daga mai bai wa shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ministan ya yaba wa hukumomin tsaro bisa gaggawar ceto waɗanda lamarin ya shafa.

  • An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa
  • Matar Dan Jaridar Da ‘Yansanda Suka Kashe A Kenya Ta Samu Diyyar Dala 78,000

An saki ‘yan jaridar biyu tare da matar Mista Alabelewe da ‘ya’yan sa biyu.

Idris ya jajanta wa iyalan biyu, inda ya ce, “Muna matuƙar godiya da abin da kuka yi. Muna sane da cewa wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da kuke yi na ganin an kuɓutar da duk waɗanda aka sace tare da sake haɗa su da iyalansu.

“Ina kira ga ‘yan Nijeriya da su ci gaba da yin imani da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da hukumomin tsaro.”

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Ya ƙara da cewa, “Hukumomin tsaron, a ƙarƙashin inuwar NSA, suna aiki tuƙuru domin ganin an kuɓutar da duk waɗanda aka sace ba tare da biyan kuɗin fansa ba.”

Da yake magana tun da farko, Malam Ribadu ya ce, an ceto mutanen biyar da aka sace ne sakamakon haɗin gwiwar da hukumomin tsaron suka yi wanda ya kai ga gudanar da bincike da ceto cikin gaggawa.

Da yake mayar da martani, ɗaya daga cikin waɗanda aka ceto, Mista Alabelewe, ya gode wa Ribadu da tawagarsa bisa gaggawar da suka yi.

Ya ce, “Aikin ceton da ya fitar da mu daga cikin daji a jiya ya ba mu fata a ƙasarmu kuma ya ba mu ƙwarin gwiwar yarda da cewa, gwamnati da gaske take wajen ganin ta magance wannan matsalar ta garkuwa da mutane.

“Ban taɓa tunanin cewa nan da mako guda da sace mu za mu kuɓuta ba. Muna godiya da gwamnati ta ɗauki mataki kuma ta tabbatar an sake mu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Garkuwa Da MutaneTa'addanciYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gdpn Sin Ya Karu Da Kashi 5% A Watanni Shida Na Farkon Bana

Next Post

Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara

Related

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

8 minutes ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

2 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

3 hours ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

12 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

13 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

14 hours ago
Next Post
Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara

Wasan Karta Na Joe Biden Game Da Xizang Ya Gaza Tun Kan Ya Fara

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.