• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

by Sulaiman
2 years ago
Boko Haram

Tsohon gwamnan jihar Neja, Dr. Muazu Babangida Aliyu, ya bayyana yadda ya fatattaki shugabannin kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau da Abu Qaqa, daga jihar Neja a wa’adinsa na farko a matsayin gwamnan jihar, inda ya ce, sun shirya mayar da jihar Hedikwatarsu.

Ya ce, shirin magance kalubalen tsaro da ke addabar Nijeriya, kamar ta’addanci da fashi da makami, shiri ne da yake bukatar tanadi mai zurfi ta hanyar kawar da adadin yara miliyan 20 da ba su zuwa makaranta su koma makaranta domin ceto Nijeriya daga matsayin kasa mafi talauci nan gaba.

  • Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar
  • Shirin Rage Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Biyan Sabon Tsarin Albashi Daga Afrilun 2024 – Minista

Dr. Aliyu ya bayyana haka ne a jihar Kaduna a karshen mako lokacin da ya bayyana a matsayin babban bako mai jawabi na shekara ta 2023, wanda cibiyar hulda da jama’a ta Nijeriya (NIPR), reshen Jihar Kaduna ta shirya.

Tsohon gwamnan ya ce, “Babban manufar gwamnati ita ce tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasarta, wanda mafi yawan gwamnonin jihohi ba sa daukarsa da muhimmanci. A matsayinka na Babban Jami’in Tsaro na jiharka, bai dace ka yi da’awar gazawa kan tsaron mutananka ba. Eh, mai yiwuwa ne jami’an hukumomin tsaro da ake turowa ba daga jiharka suka fito ba, jami’an gwamnatin tarayya ne da aka turo domin su taimaka wa jiharka.

“Kasancewarka shugaba mai kishin jama’arka, yana taimakawa sosai. A lokacin da na zama Gwamnan jihar Neja, na samu kalubalen tsaro ta hanyar wasu mutane tara da suka je wani kauye a karamar hukumar Mokwa, wadanda suka ninka a shekarar 2007 zuwa mutum 7,000 kuma suna yin fashi da makami da sace mata a yankin. Nan da nan Suka zama wata babbar runduna.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

“Na kuma gano cewa wasu gwamnoni (makwabtan Neja) da dama sun yi kokarin yin wani abu akan lamarin amma wata kila suna shakkar tunkarar Shugaban kasa. Hasali ma, jami’an hukumar shige-da-fice guda biyu da aka turo domin su binciki ayyukan kungiyar, sun rikide sun zama mambobin kungiyar. Lokacin da muka gudanar da bincike, sai muka gano cewa sama da kashi 60 cikin 100 na ‘yan kungiyar ba ‘yan Nijeriya ba ne. Asalin Shekau da Abu Qaga su ne shugabannin kungiyar. Na samu goyon bayan Marigayi Shugaban Kasa, Musa Yar’adua cewa, mu maida kowa garinshi sannan aka kai ‘yan kasashen waje iyakokin kasashensu.

“Kila wannan matakin ne ya ceto jihar Neja daga zama tushen Boko Haram. Kamar yadda muka sani, suna ziyartar gadar kogin Neja akai-akai. Babu shakka Gwamnatin Tarayya za ta goyi bayan duk wani Gwamna da ya ke kokarin sauke nauyin da ke wuyansa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma” Inji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Next Post
Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.