• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

by Bello Hamza
3 years ago
in Labarai
0
Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya musanmman ‘yan asalin yankin arewa na cigaba da yin fice a harkokin bunkasa rayuwar al’umma a sassan Duniya, ta baya-bayan nan ita ce, wata ‘yan asaloin Jihar Kano a Arewacin Nijeriya mai suna Munayah Yusuf Hassan wadda ta samu nasarar zama Mai Shari’a tare da kuma da gabatar da kara a Manyan Kotunan kasar Ingila da yankin Wales. 

Bayanin haka ya fito ne daga bakin wani shahafrraen Lauya mai zaman kansa kuma mai fafutukar kare hakkin al’umma a Nijeriya mai suna Bulama Bukarti.

  • ‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Bayanin da LEADERSHIP Hausa ta samu ya nuna cewa, Munayah ta kammala digirinta na farko ne a fannin aikin lauya daga Jami’ar Bayero da ke Kano, ta kuma halarci Babban Makarantar Lauyoyi don kwarewa tare da zama cikakkiyar lauya a Nijeriya kafin daga nan ta koma kasa Birtaniya tare da mijinta wani kwarren mai ilimin zane-zane, don cigaba da rayuwa.

Daga nan ne ta shiga harkokin ta na shari’a a kotunan kasar Birtaniya inda har hukumar shari’ar kasar ta gano irin kwazon ta aka kuma nada a wannan matsayiin.

A mastayinta na mai shari’a a manyan kotunan Birtaniya da Wales, cikin aikinta shi ne shiryarwa tare da bayar da shawara ga masu shari’a da masu neman kariya a yayin da suke fuskantar shari’a a yankin na Birtaniya da Wales gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Suna kuma shiga tare da warware harkokin shari’a da suka hada da na kasuwanci, manyan laifukka, rikicerikice da suka shafi iyali da matsalolin yau da kullun a tsakanin al’umma.

A ranar Litinin ne aka kaddamar da Munayah a wata kayatacciyar biki da aka yi a Ingila inda ta ta yi rantsuwar yin aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin Birtaniya ya samar ba tare da nuna banbancin addini ko kabilanci ba.

Munayah ta zama abin alfahari ga dukkan al’umma yankin arewacin Nijeriya musamman ganin ita ce mace ta farko da ta fara rike wannan matsayi na mai shari’a a manyan kotunan kasar Birtaniya, wannan na kuma zuwa ne a lokacin da ake ganin matan arewa a matsayin wadanda ke koma baya a fannin ilimi da harkokin cigaban al’umma.

Wannan nasara da Munayah ta samu kuma zai kara zaburar da mata da samari ‘yan arewa don su kara kaimin fuskantar karatukan su a fannoni da dama don suma su kai ga kololiyar nasara a bangaren da suka zaba wa kansu a duk inda suka samu kansu a fadin duniyar nan.

A tattanawar da ta yi da manema labarai bayan an rantsar da iya, Munayah Yusuf Hassan ta mika godiya ga Allah a bisa wannan nasarar da ta samu ta kuma gode wa mijinta da sauran ‘yan uwa a kan irin goyon bayan da suka bata a dukkan lokutta har ta kai ga samun wannan nasarar.

Muna addu’ar Allah ya sa wannan ya zama sanadiyyar daukaka ga Munayah, ‘yanuwa da abokan arzikinta da al’ummar yankin arewa dama Nijeriya gaba daya, da fatan kuma zai zama wani matakala na daukaka da abin koyi ga matasanmu na yankin Arewa don su kara kaimi a harkokin su na rayuwa daban-daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bulama BukartiIngilaLauyaMunayahWales
ShareTweetSendShare
Previous Post

Iyaye 34 Suka Yi Wa ‘Ya’yansu 48 Fyade Cikin Shekara 2

Next Post

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

9 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
Labarai

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

10 hours ago
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
Labarai

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

13 hours ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

14 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

15 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

15 hours ago
Next Post
Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.