Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta kai zagayen karshe na cin kofin Afirka (AFCON), bayan doke kasar Afirka ta Kudu a bugun da ga kai sai mai tsaron gida.
Wannan nasara da Nijeriya ta samu a wasan kusa da na karshe ya samu ne bayan an tashi wasa da 1-1, inda aka kara lokaci na mintin 30, daga bisa aka buga dukan daga kai sa mai tsaron gida.
- AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi
- AFCON 2023: Muna Alfahari Da ‘Yan Wasan Super Eagles -Tinubu
Dukkan bangarorin biyu sun kai wa guna hare-hare, sai dai babu wanda ya samu nasarar zuwa kwallo.
Nijeriya ta zura kwallaye hudu a bugun daga kai sai mai tsaron gida, inda ta zubar da kwallo guda daya, yayin da tawagar ‘yan kwallon Afirka ta Kudu suka zura kwallaye 3 bayan da suka zubar da guda biyu.
Nijeriya dai ta taka rawar gani sakamakon irin kwazon da ta nuna lokacin wannan wasa da tawagar Afirka ta Kudu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp