ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
OPEC

Bisa wani nazarin bincike da kafar yada labarai ta Reuters ta gundar ya nuna cewa, Nijeriya ta kara yawan man fetur da take hakowa zuwa ganga 70,000 a kowace rana, wanda hakan ya haura fiye da adadin da kungiyar kasashe masu arzikin man fetur OPEC+ ta sanya mata.

A cewar wannan nazarin na Reuters, a watan Fabirairun 2025, OPEC ta hako Gangannan Manfetur miliyan 26 da 74,000 a kowace rana.

  • Majalisa Ta Umarci NCC Ta Rufe Dukkanin Shafukan Intanet Na Batsa A Nijeriya
  • Hajjin Bana: NAHCON Za Ta Fara Jigilar Maniyyata A Ranar 6 Ga Mayu

Nazarin ya kara da cewa, wannan ya nuna cewa, an samu karin Gangunan Manfetur da suka kai 170,000 a kullum, idan aka kwantanta da watan Janairun 2025.

ADVERTISEMENT

A cewar binciken, hasashen da kungiyar OPEC+ ta yi a watan Fabirairu ya karu, a ya yin da Man da kasar Iran ta fitar ya karu, duk da yunkurin da kasar Amurka ta yi na dakile fitar da shi, wanda hakan ya sanya Man Nijeriya ya karu, ya kuma dara daidai da hasashen da kungiyar OPEC+.

Kasashen da suke cikin kungiyar OPEC+ da suka hada da kamar kasashen Rasha da sauran kawaye, sun nuna bukatar ganin an rage yawan Manfetur din da suke hakowa a watan Maris na 2025.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Sun nuna wannan bukatar ce, biyo bayan hasashen raguwar bukatar Manfetur din da kuma dabarar fitar da shi, daga kasashen da ba sa cikin kungiyar ta OPEC+.

Sai dai, a ranar Litinin da ta gabata kungiyar ta tsaya daram kan tsarinta na kara yawan Man da ake hakowa a watan Afirilu.

Kazalika, binciken na kafar Reuters ya kuma gano yawan adadin karuwar Man na OPEC wanda ya kai Ganguna 80,000 da suke fitowa daga kasar Iran wanda ya kai Ganuna miliyan 3.30, wannan ya kai daidai na alkaluman watan Satumba, wanda ya haura tun a 2018.

Bugu da kari, binciken ya sanar da cewa, fitar da danyan mai daga Iran ya farfado lokacin gwamnatin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden duk da takuntuman kasar Amurka, sai da karkashin shugaban kasar Amurka Donald Trump, na sabunta kokarinta.

Sauran Man na biyu na fitowa ne daga Nijeriya, inda yawan Man da take fitawa ya karu kuma yawan bukatarsa a cikin gida ta karu saboda samar da Matatar Mai ta Dangote.

Hakazalika, bincken na kafar Reuters, ya gano cewa, yawan Man da manyan kasasshe biyu da suke a cikin kungiyar OPEC wato Saudi Arabia da Irak, na su ya ragu, inda a yanzu suke hako kasa da wanda OPEC+ ta sanya masu su hako.

A cewar nazarin, man da kasashe mambobin kungiyar OPEC suka fitar a watan Fabrairun 2025 ya karu, inda Iran ke kan gaba, duk da kokarin da kasar Amurka ta yi na yunkurin dakile fitar da man.

To sai dai a ranar Litinin, ta yanke shawarar dakatar da shirin nata, inda take sa ran kara yawan man da take hakowa a watan Afrilu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Tattalin Arziki

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran

Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran

LABARAI MASU NASABA

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025
Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

November 12, 2025
Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano

November 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu

Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu

November 12, 2025
Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

November 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.