ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Umarci NCC Ta Rufe Dukkanin Shafukan Intanet Na Batsa A Nijeriya

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
NCC

Majalisar Wakilai ta Tarayya ta umarci hukumar kula da sadarwa a Nijeriya (NCC) da ta rufe dukkanin shafukan batsa a lungu da sakona a fadin kasar nan domin dakile aikata ashsha da fasadi.

Majalisar tana son kuma hukumar ta tursasa kamfanonin sadarwa da su rufe irin wadannan shafukan cikin gaggawa ba tare da bata wani lokaci ba.

  • Mutane 7 Sun Mutu, Kadarorin Miliyan 50.3 Sun Salwanta Dalilin Gobara A Kano
  • Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

Dan majalisa daga Jihar Kwara, Dalhatu Tafoki (APC), shi ne ya dauki nauyin gabatar da kudirin a zauren majalisar dokokin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Da yake jagorantar muhawara kan kudirin, Tafoki ya ce, lamarin shafukan batsa ya zama babban matsala da ake fama da shi a duniyance, ya kara da cewa kwata-kwata Nijeriya ba ta dauki wani mataki na dakile matsalar ba.

A cewarsa, Nijeriya kasa ce mai cike da addini, wadanda mafi yawan addinan da suke akwai suke yaki da irin wannan yada abubuwa na nuna tsiraici da batsa wanda suka kasance haramun a addinance.

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

Dan majalisar ya zurfafa da cewa kasashe da dama a yankin Asiya, Afrika da Gabas ta Tsakiya sun kafa dokokin da suka haramta yada abubuwan da suka shafi batsa a kasashensu.

Domin tabbatar da kudirinsa, dan majalisar Katsina ya yi tsokaci kan gargadin da masana ilimin halayyar Dan’adam da ilimin zamantakewa suka yi game da mummunan tasirin batsa ga al’umma.

A cewarsa, kallon batsa na iya janyo mutane zuwa ga tafka zina, karuwanci, da sauran ababen lalata.

“Kwararrun masana ilimin halayyar Dan’adam da na ilimin zamantakewa a fadin duniya sun gabatar da gargadi kan kallon batsa, wanda ke kaiwa ga aikata manyan badala,” ya shaida.

Kakakin Majalisar Dokoki na tarayya, Tajudeen Abbas, ya nemi mambobin majalisar da su tafka muhawara kan neman amincewa, inda kuma ‘yan majalisun sun amince da kudirin.

Majalisar ta umarci NCC da ta kakaba tara ga dukkanin kamfanin sadarwar da ya ki bin umarnin da aka bayar na toshe shafukan yanar na batsa.

Ncc
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
  • Sulaiman
    Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola
Ncc
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Labarai

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Next Post
Yadda Nijeriya Ta  Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike

Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata - Bincike

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.