• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

by Sulaiman
1 month ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gagarumin mataki na bunkasa harkokin diflomasiyya tsakanin Sin da Nijeriya, a kwanan nan ne gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) ya sanar da shirin fara watsa shirye-shirye cikin harshen Sinanci ko Mandarin a Turance. Wannan yunkuri da Darakta-Janar na VON Jibrin Ndace ya bayyana a kwanan nan yayin wata ziyarar da ya kai ofishin jakadancin Sin a Nijeriya, yana nuna wani muhimmin sauyi ne mai ma’ana da za a samu a huldar Nijeriya da Sin.

 

To amma wane muhimmanci hakan yake da shi? Amsar ita ce, ta hanyar fassara labarunta tare da watsawa da Sinanci, Nijeriya za ta bude wata sabuwar kafa ta isar da sako ga al’ummar da take da yawan jama’a a duniya. Sannan masu zuba jari na kasar Sin, da jami’an diflomasiyya, da sauran Sinawa dake da sha’awar zuba jari a tattalin arzikin Nijeriya za su rika samun sabbin bayanai kai-tsaye a cikin harshensu na asali. Wannan zai kara kawar da shingen yin cudanya da juna, kana dimbin Sinawa za su fahimci sauye-sauye da ci gaban da ake samu a Nijeriya. Kuma tabbas, wannan zai karfafa amintattun abubuwan hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu a mataki na yanki da kuma na kasa da kasa.

  • Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
  • Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Kazalika, wannan yunkuri ya nuna yadda Nijeriya ta fahimci alfanun da ke tattare da rungumar kasar Sin da gudanar da hadin gwiwa tsakanin kafofin yada labarai na kasashen biyu wanda aka rattaba wa hannu a gefen taron FOCAC da shugaba Tinubu ya halarta a birnin Beijing a bara.

Bugu da kari, kasancewar kamfanonin kasar Sin suna taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa ababen more rayuwa a Nijeriya, fara watsa shirye-shirye da Sinanci zai yi tasiri ga zurfafa hadin gwiwar sassan tattalin arzikin kasar ta hanyar zama gadar sadarwa da kara fahimtar abubuwa a kan lokaci musamman masu nasaba da bunkasa layin dogo, tituna, filayen jiragen sama, makamashi da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

A fannin noma ma, watsa shirye-shiryen da Sinanci zai taimaka wajen bayyana burin Nijeriya na fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje, musamman yadda take neman aikewa da karin kayayyakin amfanin gona zuwa babbar kasuwar kasar Sin, tare da bai wa masu ruwa da tsaki na kasar Sin damar sanin abubuwan da Nijeriya za ta iya yi, da ka’idojinta ta yadda hakan zai kara daidaita al’ummomin kasashen biyu kan dabarun kasuwanci da kara habaka musayar noma.

A halin yanzu, masana’antun kirkire-kirkiren fikira da na fina-finai, da na kayan kwalliya, da kide-kide da wake-wake suna taka rawar gani wajen harkokin al’adu da kasuwanci. Watsa shirye-shirye da Sinanci zai bai wa masu ruwa da tsaki a wannan fani na kirkire-kirkiren fikira na Nijeriya damar yin cudanya da takwarorinsu Sinawa kai-tsaye, da inganta fahimtar al’adu da yaukaka zumuncin diflomasiyya musamman ma bisa yadda kasashen biyu ke daraja al’adun gargajiya da bayar da labarai na al’mara da hikayoyi. Tabbas, wannan bangare na Nijeriya zai samu tagomashi mai albarka ta fuskar hadakar shirye-shiryen fina-finai, da bukukuwan nune-nunen, da kuma fadada samun kasuwa.

Har ila yau, yayin da Nijeriya ta shiga cikin kungiyar mawaka masu rajin ganin dunkulewar harsuna da tabbatar da damawa da kafofin watsa labaru daban-daban a duniya, watsa shirye-shiryenta da harshen Sinanci zai taimaka wa ayyukanta na diflomasiyya a fannonin tattalin arziki, da cudanyar al’adu, da hadin gwiwar manyan tsare-tsare. Don haka, watsa shirye-shiryen Nijeriya da Sinanci ba kawai bangare ne na yada labarai ba, wani babban yunkuri ne na cin moriyar samar da duniya mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

Next Post

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

4 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

5 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

6 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

7 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

8 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

10 hours ago
Next Post
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.