Wani maniyyaci ɗan Ƙasar Libya, mai suna Amer, ya samu tsaiko a filin jirgin sama yayin da yake hanyarsa ta zuwa Saudiyya aikin Hajji, inda aka samu matsala da sunansa yayin tantancewa, kuma kafin a warware lamarin, jirgin ya riga ya tashi.
Duk da haka, Amer ya ki barin filin jirgin, yana mai cewa ya yi niyyar aikin Hajji, kuma In sha Allah zai je, wanda ana cikin haka sai aka samu rahoto cewa jirgin ya samu matsala har ya dawo, amma duk da haka ba a bar shi ya shiga ba.
- Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
- Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Bayan an shawo kan damuwar har jirgin ya tashi, sai ya sake dawowa a karo na biyu da wani gyaran na daban, inda a nan ne matuƙin jirgin ya ce, lallai ba zai tashi ba sai da wannan maniyyaci ya shiga Jirgin.
Bayan an bari Amer, ya shiga jirgin, suka kama hanyarsu ta tafiya har suka sauka lafiya wanda hakan ya sa ma’aikatan jirgin suka ɗauki hoton da shi don tarihi, inda a ɗayan ɓangaren mutane da dama ke suffanta lamarin a matsayin hujjar ƙarfin niyya da ikon Allah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp