• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
ilimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani masani kuma kwararre a fannin koyo da koyarwa, sannan kuma hamshakin marubuci, Michael Omisore ya bayyana nasa dalilin na rashin samun malamai a wannan fanni na manayan darussa biyu; lissafi da kuma turanci, inda ya ce; hakan yana nuni da irin rikon sakainar kashin da ake yi wa aikin koyarwa a tsakanin al’umma.

“Darussan da dole ne sai dalibai sun samu nasara akansu, me zai sa ba za mu dauki malaman darussan, don cike wannan gurbi ba?”.

Ya ce, “Ina yin hulda da daruruwan masu nakarantu nasu na kansu a fadin tarayyar Nijeriya, wasu daga cikinsu na tambaya ta ko zan sama masu malaman Turanci gwanaye wadanda za su dauka aiki, wadansu ma har wajen zama za su ba wa malaman suka dauka.

“Don haka, me yasa ba ma daukar kwararru wadanda suke neman wannan aiki, tunda muna da wadanda suke da satifiket na kammala karatun NCE masu neman aikin yi, musamman wadabda suka karanta wadannan darussa na LIssafi da Turanci ko darussan da suke da alaka da su?”.

“Ko shakka babu, ana iya gano wadannan dalilai ta bangarori uku; yadda aka nuna lamarin ilimi a halin yanzu ba shi da wani muhimmanci, dole ne mu yi watsi da hakan, idan har ana so a dawo da martabar aikin koyarwa,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Albashin Malaman Makarantu
Kamar yadda Hausawa ke cewa, ladan malamin makaranta sai a lahira zai same shi, wannan lamari ko kadan ba haka yake ba. Dalili kuwa, ko me aka bai wa malamin makaranta; ba a biya shi ba, don kuwa ya dace a tuna da cewa shi ma yana da matsalolin da suke bukatar magani.

Kamar yadda aka sani ne cewa, babban aikin malamin makaranta shi ne koyarwa, amma albashinsa bai taka kara ya karya ba, duk da cewa abin ba a kan malamin makarantar kadai ya tsaya ba; sannan akwai wadansu abubuwa masu amfani, amma mutane na nuna kamar ba su san amfanin nasa ba.

Abin da marubucin wannan makala ke kallo shi ne, idan ana maganar albashi, shi ne abin da ya kamata ma’aikaci ya yi tinkaho da shi.

Misali, da zarar an dauki ma’aikaci aiki; a matsayinsa na malamin Turanci; a kan yi alkawari za a rika ba shi albashin Naira 50,000 a kowane wata, wannan shi ne abin da zai rika sa ran gani matsayin albashi kowane wata.

Idan ya fara aikin shekara daya zuwa biyu aka kuma samun kari, za a yi tsammanin samun karin wannan albashi, idan kuma ba a samu ba sai abubuwa su fara canzawa, musamman idan mai makarantar ya ki yin karin albashin da ya kamata ya yi, malamin na iya zuwa wani wuri daban neman wani aikin koyarwar ga kuma kwarewar da ya samu ta aiki a wannan wurin.

Saboda haka, idan ya samu wata makarantar ana iya biyan sa kimanin Naira 75,000, ko kuma albashin ya zarce na wancan makarantar da ya bari. Malaman Turanci da na Lissafi, ana matukar bukatar su idan kuma har aka dace sun san darussan sosai, suna iya samun aiki a kowane lokaci tare da albashi mai tsoka lokaci zuwa lokaci.

Omisore ya kara da cewa, a nasa ganin abu na biyu bayan wannan albashi shi ne, yadda su malaman suka dauki lamarin koyarwa a matsayin aiki ne kawai; ba abin da suka karanta a makaranta domin su rayu da shi. A cewar tasa, wannan lamari na matukar damun sa idan ya ga malamai suna neman hada kansu da Injiniyoyi ko Akantoci ko kuma Lauyoyi, duk da cewa fa su ne suka zaba wa kansu wannan fanni da suka karanta, amma kuwa sun buge da hange-hange wasu daban.

Wasu malaman na yi wa wannan lamari na koyarwa kallon albashi ne kadai, ba sa kallon albarkar da ke cikin aikin na koyarwa da kuma irin kwarewar da suke samu a kan aikin, wanda ta hakan kuma wata damar daban za ta iya samuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: rashin kishin kasaSiyasar ArewaTabarbarewar fannin ilimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS

Next Post

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

Related

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

21 hours ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 weeks ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 weeks ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

4 weeks ago
Next Post
kotu

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.