• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
ilimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani masani kuma kwararre a fannin koyo da koyarwa, sannan kuma hamshakin marubuci, Michael Omisore ya bayyana nasa dalilin na rashin samun malamai a wannan fanni na manayan darussa biyu; lissafi da kuma turanci, inda ya ce; hakan yana nuni da irin rikon sakainar kashin da ake yi wa aikin koyarwa a tsakanin al’umma.

“Darussan da dole ne sai dalibai sun samu nasara akansu, me zai sa ba za mu dauki malaman darussan, don cike wannan gurbi ba?”.

Ya ce, “Ina yin hulda da daruruwan masu nakarantu nasu na kansu a fadin tarayyar Nijeriya, wasu daga cikinsu na tambaya ta ko zan sama masu malaman Turanci gwanaye wadanda za su dauka aiki, wadansu ma har wajen zama za su ba wa malaman suka dauka.

“Don haka, me yasa ba ma daukar kwararru wadanda suke neman wannan aiki, tunda muna da wadanda suke da satifiket na kammala karatun NCE masu neman aikin yi, musamman wadabda suka karanta wadannan darussa na LIssafi da Turanci ko darussan da suke da alaka da su?”.

“Ko shakka babu, ana iya gano wadannan dalilai ta bangarori uku; yadda aka nuna lamarin ilimi a halin yanzu ba shi da wani muhimmanci, dole ne mu yi watsi da hakan, idan har ana so a dawo da martabar aikin koyarwa,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

Albashin Malaman Makarantu
Kamar yadda Hausawa ke cewa, ladan malamin makaranta sai a lahira zai same shi, wannan lamari ko kadan ba haka yake ba. Dalili kuwa, ko me aka bai wa malamin makaranta; ba a biya shi ba, don kuwa ya dace a tuna da cewa shi ma yana da matsalolin da suke bukatar magani.

Kamar yadda aka sani ne cewa, babban aikin malamin makaranta shi ne koyarwa, amma albashinsa bai taka kara ya karya ba, duk da cewa abin ba a kan malamin makarantar kadai ya tsaya ba; sannan akwai wadansu abubuwa masu amfani, amma mutane na nuna kamar ba su san amfanin nasa ba.

Abin da marubucin wannan makala ke kallo shi ne, idan ana maganar albashi, shi ne abin da ya kamata ma’aikaci ya yi tinkaho da shi.

Misali, da zarar an dauki ma’aikaci aiki; a matsayinsa na malamin Turanci; a kan yi alkawari za a rika ba shi albashin Naira 50,000 a kowane wata, wannan shi ne abin da zai rika sa ran gani matsayin albashi kowane wata.

Idan ya fara aikin shekara daya zuwa biyu aka kuma samun kari, za a yi tsammanin samun karin wannan albashi, idan kuma ba a samu ba sai abubuwa su fara canzawa, musamman idan mai makarantar ya ki yin karin albashin da ya kamata ya yi, malamin na iya zuwa wani wuri daban neman wani aikin koyarwar ga kuma kwarewar da ya samu ta aiki a wannan wurin.

Saboda haka, idan ya samu wata makarantar ana iya biyan sa kimanin Naira 75,000, ko kuma albashin ya zarce na wancan makarantar da ya bari. Malaman Turanci da na Lissafi, ana matukar bukatar su idan kuma har aka dace sun san darussan sosai, suna iya samun aiki a kowane lokaci tare da albashi mai tsoka lokaci zuwa lokaci.

Omisore ya kara da cewa, a nasa ganin abu na biyu bayan wannan albashi shi ne, yadda su malaman suka dauki lamarin koyarwa a matsayin aiki ne kawai; ba abin da suka karanta a makaranta domin su rayu da shi. A cewar tasa, wannan lamari na matukar damun sa idan ya ga malamai suna neman hada kansu da Injiniyoyi ko Akantoci ko kuma Lauyoyi, duk da cewa fa su ne suka zaba wa kansu wannan fanni da suka karanta, amma kuwa sun buge da hange-hange wasu daban.

Wasu malaman na yi wa wannan lamari na koyarwa kallon albashi ne kadai, ba sa kallon albarkar da ke cikin aikin na koyarwa da kuma irin kwarewar da suke samu a kan aikin, wanda ta hakan kuma wata damar daban za ta iya samuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: rashin kishin kasaSiyasar ArewaTabarbarewar fannin ilimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS

Next Post

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

Related

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

5 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

6 days ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 week ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

2 weeks ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

3 weeks ago
Next Post
kotu

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.