ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
kotu

Wata Babbar Kotun Jihar Bayelsa da ke zamanta a Yenagoa ta yanke wa wani mutum mai suna Baridapsi Needam mai shekaru 41 hukuncin daurin shekara 14 a gidan yari bisa samunsa da laifin yi wa ‘yarsa ciki ta hanyar fyade.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, NAN, ya ruwaito a daidai lokacin da ake shari’ar an bayyana cewa yarinyar da aka yi wa cikin ta haifi ‘ya mace.

  • Binciken Ganduje: Kotu Ta Bai Wa Alkalan Kano Sa’o’i 48 Su Yi Murabus
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Kwamishinan Shari’a na Jihar Bayelsa, kuma Babban Lauyan Gwamnati, Briyal Dambo, a kara mai lamba YHC/14C/2022, ya tuhumi wanda ake zargin da laifin aikata laifin fyade da ya saba wa sashe na 1 (1) na dokar cin zarafin jama’a ta Jihar Bayelsa ta 2021.

ADVERTISEMENT

Pere Amanda Egbuson, lauya mai shigar da kara na ma’aikatar shari’a ta Bayelsa, ya shaida wa kotun cewa bincike ya nuna cewa wanda ake zargin Needam ya fara cin zarafin ‘yarsa tun tana ‘yar shekara bakwai.
Egbuson ya ce Needam ya lalata ‘yar ne ta hanyar sanya yatsunsa a cikin al’aurarta kafin ya san ta ‘ya mace a shekarar 2020 har zuwa lokacin da ta samu ciki.

Mai shari’a D.E. Adokeme, yayin da yake yanke hukunci, ya bayyana cewa masu gabatar da kara sun gabatar da sahihiyar shaida tare da yin bincike kan sakamakon DNA, wanda ya nuna cewa kashi 99.99 cikin 100 tabbataccen rahoton cewa wanda aka yankewa hukuncin shi ne mahaifin yaron.
Kotun ta yanke hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari, inda mai gabatar da kara ya tabbatar da cewa Needam ta aikata laifin fyade.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Da yake magana bayan yanke hukuncin, Egbuson, jagoran masu shigar da kara, ya lura cewa hukuncin zai zama izna ga sauran masu aikata irin wadannan abubuwa na wuce tunanin dan dan’adam.

Ta gode wa babban mai shari’a kuma kwamishinan shari’a, Biriyai Dambo, bisa goyon bayan da ya bayar wajen ganin an gudanar da binciken DNA domin taimakawa masu gabatar da kara.

Da take mayar da martani kan wannan ci gaban, wata fitacciyar mai fafutukar yaki da cin zarafin mata, kuma wacce ta kafa gidauniyar Do Foundation, Dakta Dise Ogbise-Goddy Harry, ta yaba wa kotun bisa tabbatar da adalci.

“Gwamnatin Jihar Ta Hannun Ma’aikatar Shari’a, Ma’aikatar Harkokin Mata, Harkokin Yara da Ci Gaban jama’a da kuma kungiyar daidaita jinsi ta Jihar Bayelsa sun yi aiki mai kyau wajen ba wa wacce abin ya shafa kariya da kuma jaririyar.

Idan dai ba a manta ba Kungiyar Kare Hakkin Mata ta Jihar Bayelsa, ‘Gender Response Initiatibe Team’ (GRIT) ta mika Needman ga ‘yansanda, bayan da wani makwabcin da ya gano cewa shi ke da alhakin yi wa ‘yarsa ciki a shekarar 2022.

kotu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
kotu
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.