• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Labarai
0
Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabanni sun yi kira ga ‘yan Nijeriya musamman Musulmi da su rungumi darussa muhimmanci Maulidin haihuwar Annabi Muhammad da dabi’unsa da a wannan kakar bana.

Shugabannin sun kuma karfafa gwiwar ‘yan Nijeriya da bar wannan gagarumin biki ya zama abin koyi ga dabi’un Ma’aiki na soyayya, tausayi, da hakuri da juna, wadanda ke da matukar muhimmanci ga rayuwa a Nijeriya.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Birnin Gwari Da Giwa Bayan Kuɓutar Da Mutane 20 

A ranar Lahadi ce Musulman Nijeriya suka bi sahun Musulman duniya wajen yin murna da zagayowar ranar da aka haifi Manzon Allah Annabi Muhammad (SAW).

Shugabanni a Nijeriya sun taya al’ummar Musulman murnar Maulidi, Shugaban kasa Bola Tinubu da daukacin gwamnonin Nijeriya suka aike da sakon taya murna tare da taya al’ummar Musulmi murna bisa zagayowar Maulidin wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar, ya ce shugaban kasa Tinubu ya bukaci Musulmai da su yi amfani da wannan lokaci domin kyawawan halaye da koyarwar Manzon Allah.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su rika zurfafa game da rayuwar Annabi Muhammad, tare da bayyana kyawawan halaye kamar zaman lafiya, hakuri da juriya a yayin gudanar da bukukuwan Mauludi.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya bukaci mabiya addinin Islama da su ci gaba da zaman lafiya, yana mai cewa Annabi Muhammad ya yi rayuwar da ta dace a yi koyi da ita a wannan lokaci.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ya nuna damuwarsa kan halin kuncin da tattalin arzikin kasar ke ciki wanda ya sanya rayuwa cikin wahala ga daukacin ‘yan Nijeriya.

A cikin sakon fatan alheri na bikin Maulidin bana, wanda mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Lahadi, gwamnan ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar Allah ya kawo mana karshen wannan bala’i.

Gwamnan Jihar Filato Barr. Caleb Mutfwang ya mika sakon taya murna ga al’ummar musulmin jihar da ma sauran jihohin kasar nan na murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad.

A cikin wata sanarwar manema labarai da daraktan yada labarai da hulda da jama’a, Gyang Bere ya fitar, ya ce gwamnan ya jaddada mahimmacin Maulidi ga al’ummar Musulmi.

Shi ma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Wike ya tunatar da mazauna garin Abuja cewa ranar ba wai kawai ta kasance a matsayin biki ba ce, ta kasance koyi da kyawawan halaye da dabi’u da koyarwar Annabin da ke da tausayi da tawali’u da adalci.

Baya ga gwamnatin tarayya ta bayar da hotu a ranar Litinin 16 ga watan Satumba, bisa gimama mihimmancin wannan rana, yayin da gwamnatin Jihar Jigawa ta kuma ayyana ranar Talata 17 ga watan Satumba 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar Mauludin Annabi Muhammad (S.A.W).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MaulidiMurnaMusulmi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

Next Post

Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

8 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

9 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

12 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

14 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

17 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

18 hours ago
Next Post
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

Jerin Kasurguman 'Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.