ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Musulmi

Shugabanni sun yi kira ga ‘yan Nijeriya musamman Musulmi da su rungumi darussa muhimmanci Maulidin haihuwar Annabi Muhammad da dabi’unsa da a wannan kakar bana.

Shugabannin sun kuma karfafa gwiwar ‘yan Nijeriya da bar wannan gagarumin biki ya zama abin koyi ga dabi’un Ma’aiki na soyayya, tausayi, da hakuri da juna, wadanda ke da matukar muhimmanci ga rayuwa a Nijeriya.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Birnin Gwari Da Giwa Bayan Kuɓutar Da Mutane 20 

A ranar Lahadi ce Musulman Nijeriya suka bi sahun Musulman duniya wajen yin murna da zagayowar ranar da aka haifi Manzon Allah Annabi Muhammad (SAW).

ADVERTISEMENT

Shugabanni a Nijeriya sun taya al’ummar Musulman murnar Maulidi, Shugaban kasa Bola Tinubu da daukacin gwamnonin Nijeriya suka aike da sakon taya murna tare da taya al’ummar Musulmi murna bisa zagayowar Maulidin wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar, ya ce shugaban kasa Tinubu ya bukaci Musulmai da su yi amfani da wannan lokaci domin kyawawan halaye da koyarwar Manzon Allah.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su rika zurfafa game da rayuwar Annabi Muhammad, tare da bayyana kyawawan halaye kamar zaman lafiya, hakuri da juriya a yayin gudanar da bukukuwan Mauludi.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya bukaci mabiya addinin Islama da su ci gaba da zaman lafiya, yana mai cewa Annabi Muhammad ya yi rayuwar da ta dace a yi koyi da ita a wannan lokaci.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ya nuna damuwarsa kan halin kuncin da tattalin arzikin kasar ke ciki wanda ya sanya rayuwa cikin wahala ga daukacin ‘yan Nijeriya.

A cikin sakon fatan alheri na bikin Maulidin bana, wanda mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Lahadi, gwamnan ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar Allah ya kawo mana karshen wannan bala’i.

Gwamnan Jihar Filato Barr. Caleb Mutfwang ya mika sakon taya murna ga al’ummar musulmin jihar da ma sauran jihohin kasar nan na murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad.

A cikin wata sanarwar manema labarai da daraktan yada labarai da hulda da jama’a, Gyang Bere ya fitar, ya ce gwamnan ya jaddada mahimmacin Maulidi ga al’ummar Musulmi.

Shi ma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Wike ya tunatar da mazauna garin Abuja cewa ranar ba wai kawai ta kasance a matsayin biki ba ce, ta kasance koyi da kyawawan halaye da dabi’u da koyarwar Annabin da ke da tausayi da tawali’u da adalci.

Baya ga gwamnatin tarayya ta bayar da hotu a ranar Litinin 16 ga watan Satumba, bisa gimama mihimmancin wannan rana, yayin da gwamnatin Jihar Jigawa ta kuma ayyana ranar Talata 17 ga watan Satumba 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar Mauludin Annabi Muhammad (S.A.W).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

Jerin Kasurguman 'Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.