• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Musulmi

Shugabanni sun yi kira ga ‘yan Nijeriya musamman Musulmi da su rungumi darussa muhimmanci Maulidin haihuwar Annabi Muhammad da dabi’unsa da a wannan kakar bana.

Shugabannin sun kuma karfafa gwiwar ‘yan Nijeriya da bar wannan gagarumin biki ya zama abin koyi ga dabi’un Ma’aiki na soyayya, tausayi, da hakuri da juna, wadanda ke da matukar muhimmanci ga rayuwa a Nijeriya.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Birnin Gwari Da Giwa Bayan Kuɓutar Da Mutane 20 

A ranar Lahadi ce Musulman Nijeriya suka bi sahun Musulman duniya wajen yin murna da zagayowar ranar da aka haifi Manzon Allah Annabi Muhammad (SAW).

Shugabanni a Nijeriya sun taya al’ummar Musulman murnar Maulidi, Shugaban kasa Bola Tinubu da daukacin gwamnonin Nijeriya suka aike da sakon taya murna tare da taya al’ummar Musulmi murna bisa zagayowar Maulidin wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar, ya ce shugaban kasa Tinubu ya bukaci Musulmai da su yi amfani da wannan lokaci domin kyawawan halaye da koyarwar Manzon Allah.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su rika zurfafa game da rayuwar Annabi Muhammad, tare da bayyana kyawawan halaye kamar zaman lafiya, hakuri da juriya a yayin gudanar da bukukuwan Mauludi.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya bukaci mabiya addinin Islama da su ci gaba da zaman lafiya, yana mai cewa Annabi Muhammad ya yi rayuwar da ta dace a yi koyi da ita a wannan lokaci.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ya nuna damuwarsa kan halin kuncin da tattalin arzikin kasar ke ciki wanda ya sanya rayuwa cikin wahala ga daukacin ‘yan Nijeriya.

A cikin sakon fatan alheri na bikin Maulidin bana, wanda mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Lahadi, gwamnan ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar Allah ya kawo mana karshen wannan bala’i.

Gwamnan Jihar Filato Barr. Caleb Mutfwang ya mika sakon taya murna ga al’ummar musulmin jihar da ma sauran jihohin kasar nan na murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad.

A cikin wata sanarwar manema labarai da daraktan yada labarai da hulda da jama’a, Gyang Bere ya fitar, ya ce gwamnan ya jaddada mahimmacin Maulidi ga al’ummar Musulmi.

Shi ma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Wike ya tunatar da mazauna garin Abuja cewa ranar ba wai kawai ta kasance a matsayin biki ba ce, ta kasance koyi da kyawawan halaye da dabi’u da koyarwar Annabin da ke da tausayi da tawali’u da adalci.

Baya ga gwamnatin tarayya ta bayar da hotu a ranar Litinin 16 ga watan Satumba, bisa gimama mihimmancin wannan rana, yayin da gwamnatin Jihar Jigawa ta kuma ayyana ranar Talata 17 ga watan Satumba 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar Mauludin Annabi Muhammad (S.A.W).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
Labarai

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Next Post
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

Jerin Kasurguman 'Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

LABARAI MASU NASABA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.