ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Musulmi

Shugabanni sun yi kira ga ‘yan Nijeriya musamman Musulmi da su rungumi darussa muhimmanci Maulidin haihuwar Annabi Muhammad da dabi’unsa da a wannan kakar bana.

Shugabannin sun kuma karfafa gwiwar ‘yan Nijeriya da bar wannan gagarumin biki ya zama abin koyi ga dabi’un Ma’aiki na soyayya, tausayi, da hakuri da juna, wadanda ke da matukar muhimmanci ga rayuwa a Nijeriya.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Birnin Gwari Da Giwa Bayan Kuɓutar Da Mutane 20 

A ranar Lahadi ce Musulman Nijeriya suka bi sahun Musulman duniya wajen yin murna da zagayowar ranar da aka haifi Manzon Allah Annabi Muhammad (SAW).

ADVERTISEMENT

Shugabanni a Nijeriya sun taya al’ummar Musulman murnar Maulidi, Shugaban kasa Bola Tinubu da daukacin gwamnonin Nijeriya suka aike da sakon taya murna tare da taya al’ummar Musulmi murna bisa zagayowar Maulidin wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar, ya ce shugaban kasa Tinubu ya bukaci Musulmai da su yi amfani da wannan lokaci domin kyawawan halaye da koyarwar Manzon Allah.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su rika zurfafa game da rayuwar Annabi Muhammad, tare da bayyana kyawawan halaye kamar zaman lafiya, hakuri da juriya a yayin gudanar da bukukuwan Mauludi.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya bukaci mabiya addinin Islama da su ci gaba da zaman lafiya, yana mai cewa Annabi Muhammad ya yi rayuwar da ta dace a yi koyi da ita a wannan lokaci.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ya nuna damuwarsa kan halin kuncin da tattalin arzikin kasar ke ciki wanda ya sanya rayuwa cikin wahala ga daukacin ‘yan Nijeriya.

A cikin sakon fatan alheri na bikin Maulidin bana, wanda mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado ya fitar a ranar Lahadi, gwamnan ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar Allah ya kawo mana karshen wannan bala’i.

Gwamnan Jihar Filato Barr. Caleb Mutfwang ya mika sakon taya murna ga al’ummar musulmin jihar da ma sauran jihohin kasar nan na murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad.

A cikin wata sanarwar manema labarai da daraktan yada labarai da hulda da jama’a, Gyang Bere ya fitar, ya ce gwamnan ya jaddada mahimmacin Maulidi ga al’ummar Musulmi.

Shi ma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Wike ya tunatar da mazauna garin Abuja cewa ranar ba wai kawai ta kasance a matsayin biki ba ce, ta kasance koyi da kyawawan halaye da dabi’u da koyarwar Annabin da ke da tausayi da tawali’u da adalci.

Baya ga gwamnatin tarayya ta bayar da hotu a ranar Litinin 16 ga watan Satumba, bisa gimama mihimmancin wannan rana, yayin da gwamnatin Jihar Jigawa ta kuma ayyana ranar Talata 17 ga watan Satumba 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar Mauludin Annabi Muhammad (S.A.W).

Musulmi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

Jerin Kasurguman 'Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.