• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sinawa Ke Kokarin Sayen Hidimomi Na Haifar Da Alfanu Ga Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Sinawa Ke Kokarin Sayen Hidimomi Na Haifar Da Alfanu Ga Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu alkaluman da gwamnatin kasar Sin ta sanar da su a jiya Talata sun nuna cewa, tattalin arzikin kasar na ci gaba da farfadowa, yayin da fannin sayen hidimomi da ake yi ya karu sosai. An ce, cikin watanni 7 na farkon bana, yawan kudin da Sinawa suka kashe don neman samun hidimomi daban daban ya karu da kashi 20.3% bisa na makamancin lokacin bara. Yayin da kudin da aka kashe wajen sayen kayayyaki ya karu da kashi 7.3%.

Fannin kashe kudi da sayayya wani muhimmin bangare ne dake ba da damar ci gaban tattalin arziki, saboda haka ana sa ran ganin farfadowar bangaren sayayya a kasar Sin, ya taimakawa kokarin daidaita yanayin tafiyar hawainiya da tattalin arzikin duniya ke ciki.

  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Karyata Maganar Koma-Bayan Tattalin Arzikin Kasar

Ban da haka, sauyawar yanayin da aka samu game da fannin sayayya a kasar Sin, wanda ya dogara kan sayen kayayyaki a baya, amma yanzu haka ya fara mai da hankali kan dukkan bangarorin kayayyaki da hidimomi, za ta haifar da sabbin damammaki na samun ci gaba ga manyan kamfanonin kasa da kasa.

Haka zalika, yadda ake samun wani yanayi na tabbas dangane da manufofin tattalin arziki na Sin, shi ma wani muhimmin abu ne da manyan kamfanonin ke dauka da daraja. Yanayi na tangal-tangal da ake fama da shi a duniya ya kan sanya wasu kasashe dake yammacin duniya gyara manufofinsu a fannin tattalin arziki. Sai dai a nata bangare, kasar Sin tana kokarin tabbatar da dorewar manufofinta, ta yadda ‘yan kasuwan kasashen waje ba za su shiga cikin damuwa ba.

Dangane da batun, za mu iya daukar bangaren sayayya a matsayin wani misali, inda a wajen taron gwamnatin kasar Sin game da aikin raya tattalin arziki, da ya gudana a karshen shekarar bara, aka jaddada bukatar baiwa aikin farfado da inganta bangaren sayayya fifiko, sa’an nan zuwa bana, sai a gabatar da jerin matakai don sa kaimi ga bangaren sayayya. Ta haka ana iya ganin wani yanayi na tabbas da manufofin kasar Sin ke haifarwa tattalin arzikin duinya. Kana amfanin wadannan manufofi shi ma ya bayyana sosai. (Bello Wang)

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester City Ta Lashe Kofin Super Cup Bayan Lallasa Sevilla

Next Post

Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

16 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

16 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

18 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

21 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye

Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.