ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye

by Leadership Hausa
3 years ago
Ndume

Mai shari’a H. Mu’azu na babbar kotun birnin tarayya ya bayar da umarnin wucin gadi na hana Sanata Mohammed Ali Ndume daukar duk wani mataki na kai hari, ko muzgunawa, ko kuma barazana ga wani malamin Addinin Musulunci a Abuja, Imam Ibrahim Lawal Osama.

Kotun ta ba da umarnin ne a cikin doka mai Lamba FCT/HC/CV/7043/2023 MOTION NO: FCT/HC/M/12227/2023, sakamakon bukatar da lauyan masu shigar da kara A.L. Likko, Esq, da D.M. Yakubu Duks, Esq suka yi.

An dai zargi Sanata Ndume mai wakiltar mazabar Borno ta Kudu da bayar da umarnin kai wa Imam Osama hari, a lokacin da ake gudanar da taron addu’o’i na musamman a masallacin Apo Legislative Quarters Zone (B) da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A cikin takardar kotun da wani lauyan Nijeriya ya gani, kotun ta bayar da umarnin kamar haka:

“An ba da iznin wucin gadi da ke hana wadanda ake kara, ko dai su kansu, ko jami’ansu, ko wakilansu, da aka ba su, ko na sirri, ko duk wani wanda ya yi aiki a madadinsu ko ya samu izini daga gare su daga sake kamawa ko kuma ci gaba da tsare Imam Lawal Ibrahim Osama, ko yin duk wani aiki da zai keta hakkinshi, ‘yancin kai, hakkin mutunta dan adam har zuwa lokacin sauraren ra’ayi da kudurin da aka shigar a gaban wannan Kotun Mai Girma.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“An ba da umarnin hana masu amsa, ko da kansu, ba da izini. wakilai, kebabbu, ko duk wanda ke da niyyar yin aiki a madadinsu daga keta ko kara keta hakkinsa.

Mai kara kamar yadda sashe na 33, 34 (1) ya tabbatar 35 (1) & (4), 37, 39, 43, da 45 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya na 1999 (wanda aka yi wa gyara).

“An ba da umarnin hana wadanda ake kara da kansu, ko aka ba su, ko na sirri, ko wakilai ko duk wanda ke da niyyar yin aiki a madadinsu daga keta ko kara shiga hakkin wanda ke kara ko kuma a kan sharuddan da wannan Kotun Mai Girma ta ga ya dace a cikin kotun yanayi, har zuwa lokacin da za a yanke hukuncin wannan zama.

An dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 17 ga watan Agusta, 2023, domin sauraren wata muhimmiyar bukata.

Majiya mai tushe ta bayyana cewa, lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a yayin wani taron addu’o’i na musamman ga al’ummar kasar da aka gudanar a masallacin Apo, inda Hafizai da dama suka karanta Alkur’ani mai girma domin neman zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.”

Ana zargin Sanata Ndume da shiga masallacin ne a cikin gungun ’yan daba, kuma ya bukaci da a dakatar da addu’ar, sannan a kulle masallacin.

Hatsaniya ta barke sannan aka katse gudanar da taron karatun.

Imam Ibrahim wanda ya jagoranci addu’ar ya bukaci Sanatan da ya ci gaba da martaba da kuma girmama alfarmar wurin ibada.

Maimakon ya saurari rokon malamin, Sanatan ya yi zargin cewa ya fusata kuma ya umarci ’yan kungiyarsa su kai masa farmaki a gaban masu ibadar da suka firgita.

Malamin ya ci gaba da cewa Sanata Ndume tare da rakiyar ’yan uwansa sun yi masa mummunar wulakanci da suka hada da naushi, harbin bindiga, da kuma kalamai masu cike da barazana rikicin ya kaure ne a dai-dai lokacin da wasu masu ibada suka shiga tsakani suka yi nasarar hana Sanatan da ‘yan tawagarsa.

Malamin ya samu munanan raunuka inda nan take aka garzaya da shi asibiti domin kula da lafiyarsa.

A halin yanzu yana cikin ƙoshin lafiya amma dai tarzomar ta haddasa mashi rauni.

Nan take malamin ya kai karar lamarin a ofishin ‘yan sanda mafi kusa, kuma Sanata Ndume ya ki amsa gayyatar ‘yan sandan.

Ndume
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Sojin Nijar Ta Yi Sabbin Nade-Nade

Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.