• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Tabarbare A Cikin Shekara 10

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Tabarbare A Cikin Shekara 10
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana sun bayyana cewa, rashin iya tafiyar da arzikin Nijeriya a shekarun da suka gabata sune dalilan da suka haifar da manyan matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta a wannan lokacin.

Kafin shekarar 2015, kasar nan ta samu kudin shiga na biliyoyin daloli. Tattalin arzikin Nijeriya ya bunkasa da kashi 12.7 a tsakanin shekarun 2012 da 2013. A shekarar 2013, ya yi bunkasar da ta kai na Dala Biliyan 270 zuwa Dala Biliyan 510 wanda hakan ya sa ta zama tattalin arziki mafi girma a Afirka.

  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta
  • Da ÆŠumi-É—umi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas

Karin kashi 90 da aka samu a tattalin arzikin ya samu ne saboda shigowar bangaren kimiyyar sadarwa, fina-fnai da sauran harkokin kasuwancin da ba a bayar da rahottaninsu ba a da.

Amma kuma kididdgar da aka yi na tsawon shekara 10 wadda wata kafar sadarwar ta gudanar ya nuna yadda a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2023, aka samu gagarumin hauhawsar farashin kayayyakin masarufi a sassan Nijeriya.

Cikin manyan matakan da suka haifar da karayar tattalin arzikin Nijeriya sun kuma hada da:

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Karyewar Darajar Naira

A daidai lokacin da ake fuskantar hauhawar farashin kayan abinci sai gashi kuma an fuskanci karayar darajar naira, ana kuma rungumar takardar dala fiye da naira, abin ya kai ga gaba daya Nijeriya na dogaro ne dala wajen shigo da kayan abincin bukatar al’umma, tsananin yadda ake bukatar dala ya sanya aka fuskanci karyewar darajar nairar gaba daya.

A kididdigar da CBN ya gudanar ya nuna cewa, a shekarar 2013, ana samun dala a kan naira 159.3 daga nan ya tashi zuwa Naira 164.9 a kan dala a shekarar 2014, daga nan ya tashi zukwa naira 195.5 a shekarar 2015.

Ys kuma tashi zuwa naira 253.5 a 2016; Naira 305.7 a 2016; Naira 306 a 2017; Naira 306.9 a 2018; Naira 358 a 2020; Naira 435 a 2021; Naira 461 a shekarar 2022 daga nan ya kai naira 900 a shekarar 2023.

Farashin kayan abinci ya tashi da kashi 186

Tsadar kayan abinci a sassan kasar nan ya durkusar tare da rage abin da ‘yan Nijeriya za su iya ajiyewa daga cikin abin da suke samu a matsayin kudin shiga.

Kididdiga daga CBN ya nuna cewa an samu karuwan farashi da kashi 9.7 a shekarar 2013. Ya kuma ragu da kashi 9.4 a 2014, ya kuma sake tashi da kashi 9.8 a shekarar 2015. Ya kuma yi tashin gwauron zabo zuwa kashi 14.8 a shekarar 2016. A shekarar 2017, yana matsayin kashi 19.5, daga nan ya yi kasa zuwa kashi 14.4 a 2018 ya kuma kai kashi 13.7 a shekara 2019.

Wadannan matasalolin suka haifar da tsadar shinkafa. Shinkafa wanda abinci ne da al’umma ke amfani da shi, ya yi tashin da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan, ta yadda a halin yanzu mafi karancin albashin ma’akatan Nijeriya ba zai iya saya musu buhun shinkafa ba.

Farashin ya faro ne daga Naira 12,000 a shekarar 2013, sai ya dawo Naira 10,000 a 2014 har zuwa 2015 daga na ya tashi zuwa Naira 13,000 a 2016. A halin yanzu farashin buhun shinkafa ya tashi zuwa naira 40,000 a 2022; Naira 60,000 2023 yanzu yana fiye da Naira 70,000 a kasuwanin sassan kasar nan. Irin wannan tashin farashin ya shafi kusan dukkan kayan abincin da ake hulda da su a kasar nan, kamar fulawa, masara. Lamarin tashin farashi ya kuma shafi siminti, inda aka samu karin kashi 150 a cikin shekara 10.

Cikin abubuwan da suka haifar da tabarbarewar tattalin arzikin al’umma sun hada da karin farashin albarkatun man fetur. An sayar da litar mai a kan Naira 97 a shekarar 2013; amma ya yi tashin gwauron zabi zuwa Naira 617 a kan lita daya a halin yanzu.

Masana sun dora alhakin matsalar tattalin arzikin kasa a kan rashin aiwatar da dukkan abubuwan da aka shirya aka kuma tanada a kasafin kudi, wannan kuma yana ci gaba da jefa al’umma a cikin matsala rayuwa. A kan haka ya kamata gwamnati ta gagguta daukar matakan da suka kamata don kawo karshen wahalhalun da al’umma ke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansandan Tekun Kasar Sin Sun Kori Jirgin Ruwan Kasar Philippines Da Ya Yi Kutse Cikin Yankin Ruwan Tekun Dake Kewaye Da Tsibirin Huangyan

Next Post

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 week ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

2 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

3 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

3 weeks ago
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.