ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Tabarbare A Cikin Shekara 10

by Bello Hamza
2 years ago
Tattalin

Masana sun bayyana cewa, rashin iya tafiyar da arzikin Nijeriya a shekarun da suka gabata sune dalilan da suka haifar da manyan matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta a wannan lokacin.

Kafin shekarar 2015, kasar nan ta samu kudin shiga na biliyoyin daloli. Tattalin arzikin Nijeriya ya bunkasa da kashi 12.7 a tsakanin shekarun 2012 da 2013. A shekarar 2013, ya yi bunkasar da ta kai na Dala Biliyan 270 zuwa Dala Biliyan 510 wanda hakan ya sa ta zama tattalin arziki mafi girma a Afirka.

  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta
  • Da Ɗumi-ɗumi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas

Karin kashi 90 da aka samu a tattalin arzikin ya samu ne saboda shigowar bangaren kimiyyar sadarwa, fina-fnai da sauran harkokin kasuwancin da ba a bayar da rahottaninsu ba a da.

ADVERTISEMENT

Amma kuma kididdgar da aka yi na tsawon shekara 10 wadda wata kafar sadarwar ta gudanar ya nuna yadda a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2023, aka samu gagarumin hauhawsar farashin kayayyakin masarufi a sassan Nijeriya.

Cikin manyan matakan da suka haifar da karayar tattalin arzikin Nijeriya sun kuma hada da:

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Karyewar Darajar Naira

A daidai lokacin da ake fuskantar hauhawar farashin kayan abinci sai gashi kuma an fuskanci karayar darajar naira, ana kuma rungumar takardar dala fiye da naira, abin ya kai ga gaba daya Nijeriya na dogaro ne dala wajen shigo da kayan abincin bukatar al’umma, tsananin yadda ake bukatar dala ya sanya aka fuskanci karyewar darajar nairar gaba daya.

A kididdigar da CBN ya gudanar ya nuna cewa, a shekarar 2013, ana samun dala a kan naira 159.3 daga nan ya tashi zuwa Naira 164.9 a kan dala a shekarar 2014, daga nan ya tashi zukwa naira 195.5 a shekarar 2015.

Ys kuma tashi zuwa naira 253.5 a 2016; Naira 305.7 a 2016; Naira 306 a 2017; Naira 306.9 a 2018; Naira 358 a 2020; Naira 435 a 2021; Naira 461 a shekarar 2022 daga nan ya kai naira 900 a shekarar 2023.

Farashin kayan abinci ya tashi da kashi 186

Tsadar kayan abinci a sassan kasar nan ya durkusar tare da rage abin da ‘yan Nijeriya za su iya ajiyewa daga cikin abin da suke samu a matsayin kudin shiga.

Kididdiga daga CBN ya nuna cewa an samu karuwan farashi da kashi 9.7 a shekarar 2013. Ya kuma ragu da kashi 9.4 a 2014, ya kuma sake tashi da kashi 9.8 a shekarar 2015. Ya kuma yi tashin gwauron zabo zuwa kashi 14.8 a shekarar 2016. A shekarar 2017, yana matsayin kashi 19.5, daga nan ya yi kasa zuwa kashi 14.4 a 2018 ya kuma kai kashi 13.7 a shekara 2019.

Wadannan matasalolin suka haifar da tsadar shinkafa. Shinkafa wanda abinci ne da al’umma ke amfani da shi, ya yi tashin da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan, ta yadda a halin yanzu mafi karancin albashin ma’akatan Nijeriya ba zai iya saya musu buhun shinkafa ba.

Farashin ya faro ne daga Naira 12,000 a shekarar 2013, sai ya dawo Naira 10,000 a 2014 har zuwa 2015 daga na ya tashi zuwa Naira 13,000 a 2016. A halin yanzu farashin buhun shinkafa ya tashi zuwa naira 40,000 a 2022; Naira 60,000 2023 yanzu yana fiye da Naira 70,000 a kasuwanin sassan kasar nan. Irin wannan tashin farashin ya shafi kusan dukkan kayan abincin da ake hulda da su a kasar nan, kamar fulawa, masara. Lamarin tashin farashi ya kuma shafi siminti, inda aka samu karin kashi 150 a cikin shekara 10.

Cikin abubuwan da suka haifar da tabarbarewar tattalin arzikin al’umma sun hada da karin farashin albarkatun man fetur. An sayar da litar mai a kan Naira 97 a shekarar 2013; amma ya yi tashin gwauron zabi zuwa Naira 617 a kan lita daya a halin yanzu.

Masana sun dora alhakin matsalar tattalin arzikin kasa a kan rashin aiwatar da dukkan abubuwan da aka shirya aka kuma tanada a kasafin kudi, wannan kuma yana ci gaba da jefa al’umma a cikin matsala rayuwa. A kan haka ya kamata gwamnati ta gagguta daukar matakan da suka kamata don kawo karshen wahalhalun da al’umma ke fuskanta.

Tattalin
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.