• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tawagar Malaman Nijeriya Suka Tattauna Da Sojojin Juyin Mulkin Nijar

by Muhammad
2 years ago
Nijar

BBC ta rawaito yadda ziyarar Malaman Nijeriya ta kasance a Jamhoriyar Nijar kan wani tayin da suka yi na neman taka irin tasu rawar a dambarwar da ta ɓarke tsakanin Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar da kuma ECOWAS, Malaman addinin musulunci daga Nijeriya sun samu damar tattaunawa da shugabannin sojin Nijar.

Wani lamari na neman kaucewa zub da jini ya haɗe kan malaman Nijeriya da alokuta da dama suke yi wa juna kallon hadarin kaji.

  • Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar
  • Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar

Ƙarƙashin jagorancin Sheikh Abdullahi Bala Lau, shugaban kungiyar Izallah ta Nijeriya, malaman sun tattauna da sojojin juyin mulki na tsawon sa’o’i uku.

Sheik Bala Lau ya shaida cewa tun da fari sai da sojojin suka fara neman afuwa game da rashin sauraren tawagar tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar da Sarkin Musulmi da sauransu.

“katse wutar lantarki da hana shiga da abinci Nijar ya janyo zanga-zanga kuma matasa sun fito a ranar, gudun kada a yi musu rashin ɗa’a in sojojin shi ya sa ba su iya ba su damar tattaunawa da su ba, amma sun ce mu bayar da haƙuri a madadinsu,” kamar yadda Bala Lau ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Ta ɓangaren abin da suka cimma Malamain ya ce an samu ƙofar tattaunawar diflomasiyya, domin kuwa sojojin sun ce yanzu a shirye suke su tattauna da wakilan ECOWAS, a ko da yaushe.

“Tun daga yadda suka karɓe mu muka san cewa tafiyarmu ta yi nasara. Sun turo ministoci da Firaiministan ƙasar filin jirgin sama domin su zo su tare mu, sun kai mu kuma har fadar shugaban ƙasa da kansu.

“Mun tattauna kusan sa’a uku da su, mun tattauna kan abubuwa da dama. Mun isar da saƙo kuma mun yi nasiha domin a kiyaye zubar da jini, domin rikici idan an san farkonsa ba a san ƙarshensa ba.

“Mun ƙara nuna musu muhimmancin haɗin kai da ke tsakanin Nijeriya da Nijar, domin tarihi ne mai nisa,” in ji Sheik Bala Lau.

Ya ƙara da cewa sojojin NIjar sun yi farin ciki tare da murnar wannan ƙoƙari sun kuma nuna za su bayar da haɗin ƙai domin a samu a tattauna.

Bala Lau ya ce akwai wasu saƙonni masu yawa da za su isar ga Shugaban Najeriya da ECOWAS Bola Ahmed Tinubu waɗanda ba za su faɗu ba a waya.

Ko da aka tambaye shi game da lokacin da sojojin ke ganin ya dace a tattauna da su sai ya ce ” a ko ina aka kira su za su je kuma ko da yaushe”.

Cikin tawagar malaman akwai Sheik Bala Lau wanda ya jagoranci tawagar ya kuma gabatar da bayani.

Akwai Sheik Ƙaribullahi Nasiru Kabara da Sheik Ibrahim Dahiru Bauchi da Farfesa Khalid Sakataren ƙungiyar Jama’atu Nasril Islam da Farfesa Salisu Shehu da dai suransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Next Post
Mahangar Kungiyar Gaskiya Ta Fi Kwabo A Kan Sanata Kwankwaso Da Malam Aminu Kano

Mahangar Kungiyar Gaskiya Ta Fi Kwabo A Kan Sanata Kwankwaso Da Malam Aminu Kano

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.