ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar

by Leadership Hausa
3 years ago
Nijar

Nijeriya da Nijar ‘yan’uwan juna ne, ana kuma sa ran za su ci gaba da kasancewa a matsayin ‘yan’uwan junan. Don haka, ka da mu yarda mu rudu da jin cewa muna da karfi ko kwarewa da za ta sa mu afka wa juna ta fuska yaki, musamman idan muka yi la’akari da abin da ya faru da Kasar Ukraine, ya isa mu gane cewa ba a taba yin bari a kwashe duka.

Shugabanci ya kunshi abubuwa da dama da suka hada da samar da masalaha, tuntuba da kuma ba da damar tattaunawa domin samar da maslaha a tsanin bangarori daban-daban. Don haka, idan har muna bukatar ci gaba da zama a matsayin ‘yan’uwan juna, wajibi ne mu ci gaba da aiwatar da harkokinmu a matsayin ‘yan Afrika kuma uwa daya uba daya. kazalika, dole ne mu fahimci yadda za rika zama muna tattaunawa a tsakanin duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar

Haka zalika, ya kyautu a rika baiwa kowa ‘yancin da yake da shi tare da samar da kyakkyawar hanyar tattaunawa a lokacin da ya dace, musamman idan akwai bukatar hakan, ko da kuwa abin da ya shafi kungiyar ECOWAS ne, wannan dalili ne ma ya sa kasashen Afrikan suka shiga wannan kungiya, har ake zaben shugabanni lokaci zuwa lokaci, wanda hakan yasa aka zama kamar uwa daya uba daya.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, ya zama tilas mu koyi yadda za mu rika warware matsalolinmu a tsakanin mu na mutanen Afrika, duk wani kutse da turawan yamma za su yi a tsakanin mu da sunan taimako, babu abin da zai tsinana mana illa sake jefa mu halin ha’u’la’i. Idan muka yi la’akari da magabatan shugabanninmu na Afrika irin su marigayi Tafawa Balewa, Kwame Nkrumah Julius Nyerere, Milton Obote, Samora Mitchel, Banda, Omar Bongo, Ahamadou Ahidjo, Senghore, Mandela da sauran makamantansu, sun hada kan Afrika tamkar uwa daya uba daya.

Saboda haka, babu yadda za a yi a halin yanzu mu zauna kanmu a rarrabe sannan mu yi tsammanin samun ci gaba ko hadin kai a wadannan yankunan namu na Afrika ba. Don haka, ya kyautu kungiyar ECOWAS ta yi hobasa wajen wanzar da zaman lafiya, hadin kai da kuma kawo ci gaba ga yankunan Afrika tare da sasanta tsakanin ‘ya’yayen nata a matsayinsu na bakar fata, ba wai kasashe irin su Birtaniya, Faransa, Fotigal ko kuma kasashen Larabawa ba, a’a kawai ya kasance Afrika ita ce farko aiwatar da hakan.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Sojojin da suka yi juyin mulki a Kasar Nijar, kamar abin da ya faru ne a sauran kasashe kamar irin su; Mali, Guinea, Burkina Faso da sauran makamantansu, wanda hakan na nuna baro-baro cewa akwai alamun zalinci tare da cin amanar wadanda suka zabe su, ta hanyar rashin cika alkawarurrukan da suka yi musu, ga kuma uwa-uba bakin talaucin da suke fama da shi sakamakon rikon sakainar kashin da shugabannin nasu suka yi musu. Saboda haka, ya kyautu shugabanni su koyi magana da harshe daya, idan suka fada su rika cikawa.

A halin da ake ciki yanzu, kusan duniya baki-daya na fama da masifu iri daban daban da ya hada da matsalar zaizayar kasa, ambaliyar ruwa, yake-yake da sauran makamantansu. Wadannan dalilai kadai sun isa su sa kungiyar ECOWAS ta shiga hankalinta da kuma sauya tunani. Kasar Nijar babbar garkuwa ce ta fuskar tsaro idan aka yi la’akari da Sahara da take da shi, far mata kan haifarwa kungiyar ECOWAS da mara ido, ta hanyar rikice-rikice tare da bude kofar shigo da makamai wanda hakan kan yi sanadiyar hallaka mu baki-daya.

Don haka, muna kira da babbar murya ga kungiyar ECOWAS, da ta dubi Allah ta samar da hanyoyin warware wadannan matsalolin cikin ruwan sanyi, ba tare da amfani da karfin Soja ba.

Abraham James, Kwararre

ne a kan sadarwa da harkokin Difilomasiyya da ke Nijeriya

Nijar
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.