ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yakin Kasashen Ukraine Da Sudan Suka Janyo Karancin Irin Alkama A Jihar Gombe

by Abubakar Abba
1 year ago
Sudan

Shugaban Kungiyar Manoman Alkama, reshen Jihar Gombe; Lawan Bala Garba, ya bayyana damuwarsa kan yadda yakin da ake ci gaba da gwabzawa a Kasashen Ukraine da Sudan; ke shafar noman Alkama a fadin duniya.

Ya sanar da cewa, yakin ya kuma haifar da karancin samun Iri na Alkama, musamman a Jihar Gombe, wanda hakan ya hana manoma samun damar shuka Irin Alkama, domin noman rani.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 181, Sun Cafke 203 A Cikin Mako Guda – Hedikwatar Tsaro

Lawan ya ci gaba da cewa, kasar ta  Ukraine ita ce kan gaba a duniya wajen noman Alkamar, amma yakin da ake yi a kasar ya shafi nomanta a Jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ya sanar da cewa; Kasar Sudan wacce ita ma tana kan gaba wajen noman Alkamar a Nahiyar Afirka, yakin da ake yi a kasar ya sanya gaza yin nomanta yadda ya kamata.

A cewarsa, yake-yaken wadannan kasashe biyu, ya haifar da karancin samun Irin Alkamar a duniya, ciki har da  Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Shugaban ya ci gaba da cewa, rashin samun wadataccen Iri na Alkama a kasuwanni, ya haifar da rashin yin noman ranin a bana, duba da kakar noman ranin na bana, na kara karatowa.

A cewarsa, idan manoman ba su samu Irin Alkamar a karshen watan Dismabar 2024 ba, za su yi babbar asara; ko da kuwa daga baya an samu wadataccen Irin Alkamar.

Lawan ya ci gaba da cewa, hauhawar farashin fulawa; ya kara jawo  munanar al’amarin, duba da yadda ake sarrafa Alkamar zuwa fulawa, ba tare da an adana Irin shukarta ba.

A cewarsa, a kasuwannin Jihar Gombe, ba a samu wadatacciyar Alkamar ba, ballatana maganar samun ingantaccen Irinta da za shuka.

Ya yi nuni da cewa, bukatar da ake da ita ta Alkamar ya karu, kuma sauran Irin noman nata da suka yi saura, tuni duk an cinye su.

Sannan, ya bukaci gwamnati ta kawo dauki; musamman wajen samar da wadataccen Irin nomanta.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, noman Alkama a Jihar Gombe; na kara zama fitacce, sakamakon yadda ake samun dimbin kudaden shiga daga fannin.

Lawan  ya ci gaba da cewa, sama da manoman Alkamar 9,000 a jihar yanzu; suna noma Alkama a duk shekara; inda Karamar Hukumar Nafada, ta kasance a kan gaba.

A cewar tasa, yanzu a Karamar Hukumar ta Nafada, ana iya yin tunkahon cewa, akwai kadadar noman Alkamar sama da  3,000.

Shugaban ya kuma bukaci manoman jihar, su rungumi dabarun adana Irin Alkamar, mai makon sayar da shi; bayan kammala girbi.

A cewarsa, dole ne manoman su rika gujewa sayar da Irin da suke da shi gaba daya duk da cewa, ana samun makudan kudade idan aka sayar da Irin.

Shugaban ya kara da cewa, gazawar adana Irin; zai jawo musu gagarumar matsala a kakar noma ta gaba.

Lawan ya kuma jaddada muhimmancin gwamnati, wajen kawo daukin gaggawa; domin ganin yadda noman Alkamar ke kara lalacewa a yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Next Post
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.