• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yakin Kasashen Ukraine Da Sudan Suka Janyo Karancin Irin Alkama A Jihar Gombe

by Abubakar Abba
9 months ago
in Labarai
0
Yadda Yakin Kasashen Ukraine Da Sudan Suka Janyo Karancin Irin Alkama A Jihar Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Manoman Alkama, reshen Jihar Gombe; Lawan Bala Garba, ya bayyana damuwarsa kan yadda yakin da ake ci gaba da gwabzawa a Kasashen Ukraine da Sudan; ke shafar noman Alkama a fadin duniya.

Ya sanar da cewa, yakin ya kuma haifar da karancin samun Iri na Alkama, musamman a Jihar Gombe, wanda hakan ya hana manoma samun damar shuka Irin Alkama, domin noman rani.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 181, Sun Cafke 203 A Cikin Mako Guda – Hedikwatar Tsaro

Lawan ya ci gaba da cewa, kasar ta  Ukraine ita ce kan gaba a duniya wajen noman Alkamar, amma yakin da ake yi a kasar ya shafi nomanta a Jihar Gombe.

Kazalika, ya sanar da cewa; Kasar Sudan wacce ita ma tana kan gaba wajen noman Alkamar a Nahiyar Afirka, yakin da ake yi a kasar ya sanya gaza yin nomanta yadda ya kamata.

A cewarsa, yake-yaken wadannan kasashe biyu, ya haifar da karancin samun Irin Alkamar a duniya, ciki har da  Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Shugaban ya ci gaba da cewa, rashin samun wadataccen Iri na Alkama a kasuwanni, ya haifar da rashin yin noman ranin a bana, duba da kakar noman ranin na bana, na kara karatowa.

A cewarsa, idan manoman ba su samu Irin Alkamar a karshen watan Dismabar 2024 ba, za su yi babbar asara; ko da kuwa daga baya an samu wadataccen Irin Alkamar.

Lawan ya ci gaba da cewa, hauhawar farashin fulawa; ya kara jawo  munanar al’amarin, duba da yadda ake sarrafa Alkamar zuwa fulawa, ba tare da an adana Irin shukarta ba.

A cewarsa, a kasuwannin Jihar Gombe, ba a samu wadatacciyar Alkamar ba, ballatana maganar samun ingantaccen Irinta da za shuka.

Ya yi nuni da cewa, bukatar da ake da ita ta Alkamar ya karu, kuma sauran Irin noman nata da suka yi saura, tuni duk an cinye su.

Sannan, ya bukaci gwamnati ta kawo dauki; musamman wajen samar da wadataccen Irin nomanta.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, noman Alkama a Jihar Gombe; na kara zama fitacce, sakamakon yadda ake samun dimbin kudaden shiga daga fannin.

Lawan  ya ci gaba da cewa, sama da manoman Alkamar 9,000 a jihar yanzu; suna noma Alkama a duk shekara; inda Karamar Hukumar Nafada, ta kasance a kan gaba.

A cewar tasa, yanzu a Karamar Hukumar ta Nafada, ana iya yin tunkahon cewa, akwai kadadar noman Alkamar sama da  3,000.

Shugaban ya kuma bukaci manoman jihar, su rungumi dabarun adana Irin Alkamar, mai makon sayar da shi; bayan kammala girbi.

A cewarsa, dole ne manoman su rika gujewa sayar da Irin da suke da shi gaba daya duk da cewa, ana samun makudan kudade idan aka sayar da Irin.

Shugaban ya kara da cewa, gazawar adana Irin; zai jawo musu gagarumar matsala a kakar noma ta gaba.

Lawan ya kuma jaddada muhimmancin gwamnati, wajen kawo daukin gaggawa; domin ganin yadda noman Alkamar ke kara lalacewa a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

Next Post

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

Related

Sudan
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

2 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

2 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

3 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

3 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

4 hours ago
Sudan
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

5 hours ago
Next Post
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

LABARAI MASU NASABA

Sudan

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Sudan

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.