ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yakin Kasashen Ukraine Da Sudan Suka Janyo Karancin Irin Alkama A Jihar Gombe

by Abubakar Abba
2 years ago
Sudan

Shugaban Kungiyar Manoman Alkama, reshen Jihar Gombe; Lawan Bala Garba, ya bayyana damuwarsa kan yadda yakin da ake ci gaba da gwabzawa a Kasashen Ukraine da Sudan; ke shafar noman Alkama a fadin duniya.

Ya sanar da cewa, yakin ya kuma haifar da karancin samun Iri na Alkama, musamman a Jihar Gombe, wanda hakan ya hana manoma samun damar shuka Irin Alkama, domin noman rani.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 181, Sun Cafke 203 A Cikin Mako Guda – Hedikwatar Tsaro

Lawan ya ci gaba da cewa, kasar ta  Ukraine ita ce kan gaba a duniya wajen noman Alkamar, amma yakin da ake yi a kasar ya shafi nomanta a Jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ya sanar da cewa; Kasar Sudan wacce ita ma tana kan gaba wajen noman Alkamar a Nahiyar Afirka, yakin da ake yi a kasar ya sanya gaza yin nomanta yadda ya kamata.

A cewarsa, yake-yaken wadannan kasashe biyu, ya haifar da karancin samun Irin Alkamar a duniya, ciki har da  Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Shugaban ya ci gaba da cewa, rashin samun wadataccen Iri na Alkama a kasuwanni, ya haifar da rashin yin noman ranin a bana, duba da kakar noman ranin na bana, na kara karatowa.

A cewarsa, idan manoman ba su samu Irin Alkamar a karshen watan Dismabar 2024 ba, za su yi babbar asara; ko da kuwa daga baya an samu wadataccen Irin Alkamar.

Lawan ya ci gaba da cewa, hauhawar farashin fulawa; ya kara jawo  munanar al’amarin, duba da yadda ake sarrafa Alkamar zuwa fulawa, ba tare da an adana Irin shukarta ba.

A cewarsa, a kasuwannin Jihar Gombe, ba a samu wadatacciyar Alkamar ba, ballatana maganar samun ingantaccen Irinta da za shuka.

Ya yi nuni da cewa, bukatar da ake da ita ta Alkamar ya karu, kuma sauran Irin noman nata da suka yi saura, tuni duk an cinye su.

Sannan, ya bukaci gwamnati ta kawo dauki; musamman wajen samar da wadataccen Irin nomanta.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, noman Alkama a Jihar Gombe; na kara zama fitacce, sakamakon yadda ake samun dimbin kudaden shiga daga fannin.

Lawan  ya ci gaba da cewa, sama da manoman Alkamar 9,000 a jihar yanzu; suna noma Alkama a duk shekara; inda Karamar Hukumar Nafada, ta kasance a kan gaba.

A cewar tasa, yanzu a Karamar Hukumar ta Nafada, ana iya yin tunkahon cewa, akwai kadadar noman Alkamar sama da  3,000.

Shugaban ya kuma bukaci manoman jihar, su rungumi dabarun adana Irin Alkamar, mai makon sayar da shi; bayan kammala girbi.

A cewarsa, dole ne manoman su rika gujewa sayar da Irin da suke da shi gaba daya duk da cewa, ana samun makudan kudade idan aka sayar da Irin.

Shugaban ya kara da cewa, gazawar adana Irin; zai jawo musu gagarumar matsala a kakar noma ta gaba.

Lawan ya kuma jaddada muhimmancin gwamnati, wajen kawo daukin gaggawa; domin ganin yadda noman Alkamar ke kara lalacewa a yankin.

Sudan
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.