• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Sace Fasinjojin Motar Bas 20 A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
‘Yan Ƙwadago Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai-baba-ta-gani A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun yi awon gaba da fasinjoji 20 a kan hanyar da ta hada Mariga da Karamar Hukumar Kontagora a Jihar Neja.

 

Fasinjojin na tafiya ne a kan titin, yayin da ‘yan fashin, suka sauke su daga mota suka tilasta musu shiga wani dajin da ke kusa.

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Singapore Da Azerbaijan
  • An Kama Wasu Ƴansanda Kan Zargin Kisan Ɗalibin Jami’ar Kwara

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin-Daji, mai wakiltar mazabar Mariga, ya tabbatar da sace mutanen a ranar Alhamis. Kalaman nasa sun biyo bayan kin amincewar da sojoji suka yi na kai hare-haren ‘yan bindiga a wuraren horar da sojoji da suka hada da Kananan Hukumomin Kontagora da Mariga.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Ya shaida wa manema labarai lamarin ya faru ne a yayin da ‘yan bindiga suka tare hanyar Mariga zuwa Kontagora tsakanin Baban-Lamba da Beri.

 

Shugaban majalisar ya kara da cewa iyalan wadanda aka yi garkuwa da su a baya sun rika karbar kudaden fansa a wani yanki dazuzzuka, wanda aka ruwaito a kusa da filin horar da sojoji. Wadanda abin ya shafa sun shaida wa iyalansu cewa an tsare su ne a kusa da Barikin Sojoji na Kontagora.

 

Sarkin-Daji ya bukaci sojoji da su yi aiki da sahihan bayanai tare da kawar da ‘yan fashin daga yankin, yana mai cewa, “Fasinjojin da aka yi garkuwa da su a ranar Alhamis a hanyar Mariga zuwa Kontagora, an kai su dajin guda.”

 

Shugaban majalisar ya jaddada cewa, a matsayinsu na wakilan jama’a, ‘yan majalisar su kan sami amsa kai tsaye daga ‘yan mazabar kan wahalhalun da suke ciki, kuma suna yin nazari sosai kan wadannan batutuwa kafin su gabatar da su gaban majalisar.

 

Yayin da yake amincewa da karfin soja na yaki da ‘yan fashi, ya yi gargadi game da watsi da korafe-korafen mazabar.

 

Ya bukaci gwamnatin tarayya da hukumomin da abin ya shafa da su shawo kan wadannan matsalolin, inda ya bayyana cewa al’ummomin yankin na zargin wuraren horar da sojoji sun zama mafakar ‘yan bindiga.

 

“Hatta wadanda aka sako bayan an biya kudin fansa sun bayyana cewa an tsare su ne a gaban Barikin Sojojin Kontagora,” a cewar Sarkin-Daji.

 

“Sojoji su tabbatar da bayanan wadanda abin ya shafa kan su magance matsalar, maimakon yin watsi da maganganun da ‘yan majalisar suka yi.”

 

Duk da korar da sojoji suka yi a baya na furucin dan Majalisar daya, ‘yan bindiga sun tare hanyar Baban-Lamba zuwa Beri inda suka yi awon gaba da fasinjoji sama da 20 tare da mayar da su daji guda.

 

Shugaban majalisar ya yi kira ga sojoji da su kori miyagu daga yankin tare da jaddada cewa majalisar za ta ci gaba da wayar da kan jama’a don tabbatar da gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki sun fahimci halin da jama’a ke ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BindigaNeja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Halarci Taron Haɗin Gwiwar Larabawa Da Musulmai A Saudiya

Next Post

Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

13 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

56 minutes ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

2 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

4 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

5 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

6 hours ago
Next Post
Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.