• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Sace Fasinjojin Motar Bas 20 A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
12 months ago
Bindiga

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun yi awon gaba da fasinjoji 20 a kan hanyar da ta hada Mariga da Karamar Hukumar Kontagora a Jihar Neja.

 

Fasinjojin na tafiya ne a kan titin, yayin da ‘yan fashin, suka sauke su daga mota suka tilasta musu shiga wani dajin da ke kusa.

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Singapore Da Azerbaijan
  • An Kama Wasu Ƴansanda Kan Zargin Kisan Ɗalibin Jami’ar Kwara

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin-Daji, mai wakiltar mazabar Mariga, ya tabbatar da sace mutanen a ranar Alhamis. Kalaman nasa sun biyo bayan kin amincewar da sojoji suka yi na kai hare-haren ‘yan bindiga a wuraren horar da sojoji da suka hada da Kananan Hukumomin Kontagora da Mariga.

 

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

Ya shaida wa manema labarai lamarin ya faru ne a yayin da ‘yan bindiga suka tare hanyar Mariga zuwa Kontagora tsakanin Baban-Lamba da Beri.

 

Shugaban majalisar ya kara da cewa iyalan wadanda aka yi garkuwa da su a baya sun rika karbar kudaden fansa a wani yanki dazuzzuka, wanda aka ruwaito a kusa da filin horar da sojoji. Wadanda abin ya shafa sun shaida wa iyalansu cewa an tsare su ne a kusa da Barikin Sojoji na Kontagora.

 

Sarkin-Daji ya bukaci sojoji da su yi aiki da sahihan bayanai tare da kawar da ‘yan fashin daga yankin, yana mai cewa, “Fasinjojin da aka yi garkuwa da su a ranar Alhamis a hanyar Mariga zuwa Kontagora, an kai su dajin guda.”

 

Shugaban majalisar ya jaddada cewa, a matsayinsu na wakilan jama’a, ‘yan majalisar su kan sami amsa kai tsaye daga ‘yan mazabar kan wahalhalun da suke ciki, kuma suna yin nazari sosai kan wadannan batutuwa kafin su gabatar da su gaban majalisar.

 

Yayin da yake amincewa da karfin soja na yaki da ‘yan fashi, ya yi gargadi game da watsi da korafe-korafen mazabar.

 

Ya bukaci gwamnatin tarayya da hukumomin da abin ya shafa da su shawo kan wadannan matsalolin, inda ya bayyana cewa al’ummomin yankin na zargin wuraren horar da sojoji sun zama mafakar ‘yan bindiga.

 

“Hatta wadanda aka sako bayan an biya kudin fansa sun bayyana cewa an tsare su ne a gaban Barikin Sojojin Kontagora,” a cewar Sarkin-Daji.

 

“Sojoji su tabbatar da bayanan wadanda abin ya shafa kan su magance matsalar, maimakon yin watsi da maganganun da ‘yan majalisar suka yi.”

 

Duk da korar da sojoji suka yi a baya na furucin dan Majalisar daya, ‘yan bindiga sun tare hanyar Baban-Lamba zuwa Beri inda suka yi awon gaba da fasinjoji sama da 20 tare da mayar da su daji guda.

 

Shugaban majalisar ya yi kira ga sojoji da su kori miyagu daga yankin tare da jaddada cewa majalisar za ta ci gaba da wayar da kan jama’a don tabbatar da gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki sun fahimci halin da jama’a ke ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya
Manyan Labarai

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa
Manyan Labarai

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Next Post
Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.