ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Sace Fasinjojin Motar Bas 20 A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Bindiga

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun yi awon gaba da fasinjoji 20 a kan hanyar da ta hada Mariga da Karamar Hukumar Kontagora a Jihar Neja.

 

Fasinjojin na tafiya ne a kan titin, yayin da ‘yan fashin, suka sauke su daga mota suka tilasta musu shiga wani dajin da ke kusa.

ADVERTISEMENT
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Singapore Da Azerbaijan
  • An Kama Wasu Ƴansanda Kan Zargin Kisan Ɗalibin Jami’ar Kwara

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin-Daji, mai wakiltar mazabar Mariga, ya tabbatar da sace mutanen a ranar Alhamis. Kalaman nasa sun biyo bayan kin amincewar da sojoji suka yi na kai hare-haren ‘yan bindiga a wuraren horar da sojoji da suka hada da Kananan Hukumomin Kontagora da Mariga.

 

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Ya shaida wa manema labarai lamarin ya faru ne a yayin da ‘yan bindiga suka tare hanyar Mariga zuwa Kontagora tsakanin Baban-Lamba da Beri.

 

Shugaban majalisar ya kara da cewa iyalan wadanda aka yi garkuwa da su a baya sun rika karbar kudaden fansa a wani yanki dazuzzuka, wanda aka ruwaito a kusa da filin horar da sojoji. Wadanda abin ya shafa sun shaida wa iyalansu cewa an tsare su ne a kusa da Barikin Sojoji na Kontagora.

 

Sarkin-Daji ya bukaci sojoji da su yi aiki da sahihan bayanai tare da kawar da ‘yan fashin daga yankin, yana mai cewa, “Fasinjojin da aka yi garkuwa da su a ranar Alhamis a hanyar Mariga zuwa Kontagora, an kai su dajin guda.”

 

Shugaban majalisar ya jaddada cewa, a matsayinsu na wakilan jama’a, ‘yan majalisar su kan sami amsa kai tsaye daga ‘yan mazabar kan wahalhalun da suke ciki, kuma suna yin nazari sosai kan wadannan batutuwa kafin su gabatar da su gaban majalisar.

 

Yayin da yake amincewa da karfin soja na yaki da ‘yan fashi, ya yi gargadi game da watsi da korafe-korafen mazabar.

 

Ya bukaci gwamnatin tarayya da hukumomin da abin ya shafa da su shawo kan wadannan matsalolin, inda ya bayyana cewa al’ummomin yankin na zargin wuraren horar da sojoji sun zama mafakar ‘yan bindiga.

 

“Hatta wadanda aka sako bayan an biya kudin fansa sun bayyana cewa an tsare su ne a gaban Barikin Sojojin Kontagora,” a cewar Sarkin-Daji.

 

“Sojoji su tabbatar da bayanan wadanda abin ya shafa kan su magance matsalar, maimakon yin watsi da maganganun da ‘yan majalisar suka yi.”

 

Duk da korar da sojoji suka yi a baya na furucin dan Majalisar daya, ‘yan bindiga sun tare hanyar Baban-Lamba zuwa Beri inda suka yi awon gaba da fasinjoji sama da 20 tare da mayar da su daji guda.

 

Shugaban majalisar ya yi kira ga sojoji da su kori miyagu daga yankin tare da jaddada cewa majalisar za ta ci gaba da wayar da kan jama’a don tabbatar da gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki sun fahimci halin da jama’a ke ciki.

Bindiga
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Bindiga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.