ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Sace Fasinjojin Motar Bas 20 A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Bindiga

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun yi awon gaba da fasinjoji 20 a kan hanyar da ta hada Mariga da Karamar Hukumar Kontagora a Jihar Neja.

 

Fasinjojin na tafiya ne a kan titin, yayin da ‘yan fashin, suka sauke su daga mota suka tilasta musu shiga wani dajin da ke kusa.

ADVERTISEMENT
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Singapore Da Azerbaijan
  • An Kama Wasu Ƴansanda Kan Zargin Kisan Ɗalibin Jami’ar Kwara

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin-Daji, mai wakiltar mazabar Mariga, ya tabbatar da sace mutanen a ranar Alhamis. Kalaman nasa sun biyo bayan kin amincewar da sojoji suka yi na kai hare-haren ‘yan bindiga a wuraren horar da sojoji da suka hada da Kananan Hukumomin Kontagora da Mariga.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Ya shaida wa manema labarai lamarin ya faru ne a yayin da ‘yan bindiga suka tare hanyar Mariga zuwa Kontagora tsakanin Baban-Lamba da Beri.

 

Shugaban majalisar ya kara da cewa iyalan wadanda aka yi garkuwa da su a baya sun rika karbar kudaden fansa a wani yanki dazuzzuka, wanda aka ruwaito a kusa da filin horar da sojoji. Wadanda abin ya shafa sun shaida wa iyalansu cewa an tsare su ne a kusa da Barikin Sojoji na Kontagora.

 

Sarkin-Daji ya bukaci sojoji da su yi aiki da sahihan bayanai tare da kawar da ‘yan fashin daga yankin, yana mai cewa, “Fasinjojin da aka yi garkuwa da su a ranar Alhamis a hanyar Mariga zuwa Kontagora, an kai su dajin guda.”

 

Shugaban majalisar ya jaddada cewa, a matsayinsu na wakilan jama’a, ‘yan majalisar su kan sami amsa kai tsaye daga ‘yan mazabar kan wahalhalun da suke ciki, kuma suna yin nazari sosai kan wadannan batutuwa kafin su gabatar da su gaban majalisar.

 

Yayin da yake amincewa da karfin soja na yaki da ‘yan fashi, ya yi gargadi game da watsi da korafe-korafen mazabar.

 

Ya bukaci gwamnatin tarayya da hukumomin da abin ya shafa da su shawo kan wadannan matsalolin, inda ya bayyana cewa al’ummomin yankin na zargin wuraren horar da sojoji sun zama mafakar ‘yan bindiga.

 

“Hatta wadanda aka sako bayan an biya kudin fansa sun bayyana cewa an tsare su ne a gaban Barikin Sojojin Kontagora,” a cewar Sarkin-Daji.

 

“Sojoji su tabbatar da bayanan wadanda abin ya shafa kan su magance matsalar, maimakon yin watsi da maganganun da ‘yan majalisar suka yi.”

 

Duk da korar da sojoji suka yi a baya na furucin dan Majalisar daya, ‘yan bindiga sun tare hanyar Baban-Lamba zuwa Beri inda suka yi awon gaba da fasinjoji sama da 20 tare da mayar da su daji guda.

 

Shugaban majalisar ya yi kira ga sojoji da su kori miyagu daga yankin tare da jaddada cewa majalisar za ta ci gaba da wayar da kan jama’a don tabbatar da gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki sun fahimci halin da jama’a ke ciki.

Bindiga
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Bindiga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.