Sabani a kan wata sabuwar dokar zabe a Saliyo ya haddasa fada a tsakanin ‘yan majalisar dokokin kasar, inda suka rika bai wa hammata iska a zauren majalisar.
Abin da masu amfani da shafin twitter ‘yan saliyo suka kira hatsaniya an ga yadda ake ta kutufar juna a zauren majalisar.
- Kotun Daukaka Kara Ta Dawo Wa Da Aishatu Binani Takararta Ta Gwamna A Adamawa
- Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume
An rika wurgi da sandar iko ta majalisar daga nan zuwa can.
Wani dan jarida ya ce daga nan ne kuma sai jami’an tsaro suka shiga tsakani inda suka yi waje da wasu daga cikin ‘yan majalisar.
BBC Hausa ta ce rikicin ya barke ne tsakanin ‘yan majalisar jam’iyya mai mulki da kuma na jam’iyyun hamayya a kan wani kuduri na sanya wakilci a hukumar zaben kasar daidai da karfin kowace jam’iyya a kan shirin zabukan da za a yi a shekara mai zuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp