• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kwamitin Rundunar Soji a Majalisar Dattawa, Sanata Muhammad Ndume ya bayyana cewa akwai bukatar a binciki Bankin Ci Gaban Nijeriya watau Development Bank of Nigeria (DBN) da Gwamnatin Tarayya ta kafa domin taimakawa kananan masana’antu da `yan Kasuwa sakamakon zargin gudanar da al’amura ta hanyar da bata dace ba.

  • Buhari Ya Halarci Wajen Kaddamar Da Hako Man Fetur A Bauchi 

Ndume wanda ya kasance mamba a cikin wani kwamitin na wucin gadi na mutane bakwai da Sanata Muhammad Sani Musa 313 ke jagoranta a Majalisar Dattawan Tarayyar, ya yi nuni da cewa a wani binciken da suka yi alamu na nuni da cewa kwalliya ba ta biya kuɗin sabulu ba.

Ya kara da cewa an kawo Kudirin Dokar ne domin a binciki Bankin ta DBN wanda Gwamnatin Tarayya ta kafa saboda tabbatar da an taimaka wa kananan `yan Kasuwa da masana’antu domin su samu tallafi mai sauki ta yadda za su farfado ko su kafa kananan masana’antu wanda yake da mahimmaci ga masu kananan karfi domin idan aka farfado da wannan `yan Kasuwa da masana’antu shi ne za a iya farfado da tattalin Arzikin Kasar.

Ya ce “amma abun takaici shi ne mun lura a cikin wani bincike cewa Bankin DBN a cikin shekarar 2021, ta rabar da kudi kusan kimanin rabin Tiriliyan, amma abun takaici shi ne inda talauci ya fi katutu kuma inda ake bukatar a farfado da kananan masana’antu ba su samu ko rabin abin da suka rabar ba.

“Na gano cewa Jihar Legas kadai a cikin Kudi naira Biliyan 483 sun samu kashi 47% amma sauran shiyyar Kudu maso yamma sun samu kashi 10 wanda gaba daya kudin ya kama naira Tiriliyan 274 a yayin da daga cikin Jihohi shida na Kudu maso yamma, ita Jihar Legas kadai ke da Kudi kimanin naira Biliyan 227 amma sauran Jihohin biyar ke da kashi 10.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

“Haka Kudu maso Kudu sun samu kashi 17 da ya kama Naira Biliyan 81, amma gaba dayan Arewa da ke da Jahohi 19 sun samu kashi 11 wanda ya kama kimanin naira Biliyan 53, domin a shiyyar Arewa maso gabas ta samu kashi 5 wato naira Biliyan 24, sai shiyyar Arewa maso yamma ta samu kashi daya wato Naira Biliyan 4,820.

 

“Makasudin kafa wannan Bankin shi ne don ta taimaka wa kananan `yan Kasuwa da masana’antu wanda sune ke fannin Noma, kasuwanci, sufuri amma sai muka ga sun dauki kashi 42 na kudin sun ba masu harkar mai.

 

“Kudin da aka bayar ga shiyyoyin 6 bashi ne ake bayarwa mai sassauci don farfado da tattalin Arzikin Kasa ta hanyar Bankin don ita Bankin da za ta bayar, ba tana bayarwa ba ne don riba sai don a taimaka.

“Misali a Jihar Kano da Sokoto an rufe masana’antu da yawa don ba Kudin da za a farfado da su, shi ne ya sa ake so a basu wannan kudin da zai zamanto ba za a kuntata musu ba, toh amma kwalliya ba ta biya kuɗin sabulu ba.

Acewarsa, akwai bukatar a yi bincike don sanin shin nawa ne Kudin, mai yasa aka rabar da kudin haka, meye za ayi don tabbatar cewa dalilin da ya sa aka kafa wannan Banki da kuma tabbatar da cewa Kudaden da ake rabar sun je ga hannun wadanda ya kamata, kuma `yan Nijeriya su gani a kasa ta hanyar tabbatar da cewa kananan masana’antu na tasowa ta hanyar taimakon wannan Banki tunda a bisa wannan dalilin ya sa aka kafa Bankin na DBN.

“Kuma akwai Bankin Kasuwanci (BOI), NIRSAL ta CBN da Gwamnatin Tarayya da suka sha fitar da wadansu hanyoyin da tsari don taimaka wa `yan Nijeriya talakawa amma har yanzu ba a gani a Kasa ba saboda matsalar wadanda aka saka su su yi aikin ya sa muke son mu yi bincike a Majalisar domin idan da akwai wadanda suka hana ruwa gudu, sai a san yadda za a yi a kawar da su domin a samu tsari mai kyau a kan abin da ake bukata.

“An hada kwamitin wucin Gadi na mutum bakwai, an saka ni member kuma Inshaa Allah za mu tabbatar da cewa an yi abun da ya dace don tabbatar da cewa `yan Nijeriya sun ga abin da aka yi tare da tabbatar cewa an yi maganin matsalar.

“A yanzu talauci ya addabi `yan Nijeriya musamman Arewa. A kiyasi, Jihar Kebbi na fama da talauci kimanin kashi 86, Jihar Gombe 77, Jihar Bauchi 87, Jihar Taraba 78, Jihar Zamfara kashi 80, sannan kusan rabin Jihar Filato na fama da talauci, haka sama da rabin `yan Jihar Ebonyi su ma suna fama da talauci, shi yasa ni a matsayin wakili na kai wannan lamarin gaban Majalisar don a yi wa tubkar hanci, a yi maganin lamarin kuma `yan uwana `yan majalisar sun karbi abun hannu biyu-biyu, don haka suka bani goyon baya.” Inji Ndume


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Ganawa Tsakanin Ministocin Tsaron Kasashen Sin Da Amurka 

Next Post

Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

11 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

13 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

15 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

17 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

19 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

19 hours ago
Next Post
Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.