• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za A Rage Ricikin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya -Miyetti Allah

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Za A Rage Ricikin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya -Miyetti Allah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Fulani makiyya ta kasa reshen jihar Bauchi Miyetti Allah ta bayyana cewa, dawo da amfani da burtaloli kasar nan ne kawai mafita kan kawo karshen ricikin da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin manoma da makiyyan kasar nan.

Shugaban kungiyar reshen jihar Alhaji Sadikue Ibrahim Ahmed a wata hirarsa da manema labarai a jihar Bauchi, inda shugaban ya yi nuni da cewa, batar da burtaloli kasar nan ne Fulani makiyya komawa cikin jeji.

  • Yadda Aka Yi Fito-na-fito Da Masu Gidaje Da Jami’an Rusau A Kano

Sadikue ya bayyana cewa, hakan ya jano fulanin makiyaya suke yin kaura zuwa jeji a lokacin rani don su samu su ciyar da dabbobin su.

A cewarsa, amma a yau dabbobin na makiyya sun kasance suna yin kiwo a kan tituna wasu kuma suna kwana a cikin kwangaye.

“Hakan ya jano fulanin makiyaya suke yin kaura zuwa jeji a lokacin rani don su samu su ciyar da dabbobin su.”

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Ya sanar da cewa, tun kafin zuwan turawa cikin kasar nan, akwai burtaloli da dabbobin makiyan ke bi, inda ya yi nuni da cewa, hatta wasu guaren da aka kebewa makiyyan wasu mutanen sun yi gine-gine akansu
Shugaban kungiyar ya bayana cewa, sai idan gwamnati ta dawo da burtulolin ne kamar yadda ake da su a jamhuriyya ta biyu a kasar nan, sannan za a samu sa’ida kan yawan samu rikece-rikice a tsakanin makiyya da manoma.

“Tun kafin zuwan turawa cikin kasar nan, akwai burtaloli da dabbobin makiyan ke bi, inda ya yi nuni da cewa, hatta wasu guaren da aka kebewa makiyyan wasu mutanen sun yi gine-gine akansu.”

Ya sanar da cewa, irin cin kashin da ake yiwa makiyya a kasar nan abin takaici ne, inda ya kara da cewa, da yawan su an kore su daga guraren da kakaknsu suke tun asali kusan sama da shakaru 100. duk shekara, ana yawan samu rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani makiyya a kasar nan.

A wani labarin kuwa, masana a fannin noman Rogo a kasar nan sun bayyana cewa, daga cikin tan miliyan 53 na Rogon da ake noma wa a Nijeriya a duk shekara, sama da kashi 90 a cikin dari ana sarrafa Rogon zuwa sauran wasu nau’ukan abinci.

A cewarsu, kiididdga ce ta tabbatar da wannan adadin, inda masanan suka kara da cewa, fannin na noman Rogon ya taimaka wajen samar wa da miliyoyin ‘yan Nijeriya aikin yi idan kuma aka inganta fannin, zai samar fiye da hakan.

Masanan sun sanar da hakan ne a a taron kara wa juna sani da suka gudanar a Babban Birnin Tarayyar Abuja, inda kuma suka yi nuni da cewa,kokarin da gwamtin tarayya ke ci gaba da yi na sake farfado noman na Rogo a Nijeriya, musamman kan daukain da Babban Bankin Nijeriya CBN ke samar wa a fannin, inda ya yi nuni da cewa, CBN ya bayar da gagarumar gudunawa wajen bunkasa fannin na noman Rogo a kasar nan.

“Kokarin na gwamtin tarayya ga fannin abin yaba wa ne matuka, musamman ganin cewa, nomansa na daya daga cikin amfanin gona da ke kara karfafa tattalin arzikin duniya”.

A cewar masanan, Nijeriya ce ke a kan gaba wajen noman Rogo, inda suka bayyana cewa, kasar na samar da kimanin tan miliyan 53 na Rogo a shekarar 2018 tare da kuma ta ke samar da akalla tan 7.7 ako wacce kadada daya, idan aka kwatanta da tan 23.4 da kuma tan 22.2 da ake samarwa a kasashen in Indonesiya da Thailand.

Masanan sun sanar cewa, ci gaba da sake farfado noman na Rogo a Nijeriya da gwamnati ke ci gaba da yi, musamman ta hanyar yin amfani da daukin da kan Babban Bankin Nijeriya ya kara taimaka wa matuka wajen kara bunkasa fannin na noman Rogon a kasar, da Kara fitar da shi zuwa kasuwar duniya, inda kuma hakan ya kara samar wa gwamnatin kasar kudaden shiga masu dimbin yawa.

“Nijeriya ce ke a kan gaba wajen noman Rogo, inda suka bayyana cewa, kasar na samar da kimanin tan miliyan 53 na Rogo a shekarar 2018 tare da kuma ta ke samar da akalla tan 7.7 ako wacce kadada daya, idan aka kwatanta da tan 23.4 da kuma tan 22.2 da ake samarwa a kasashen in Indonesiya da Thailand”.

Masanan sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi dukkan mai yuwa wajen kara samar da masu zuba jari a fannin na noman Rogon a kasar, musamman idan aka yi la’akari da irin dimbin kudaden shiga da fannin ke samar wa da manoman Rogon a kasar, inda kuma suka yi yi nuni da cewa, hakan zai kara taimaka wa wajen kara samar da ayyukan yi ga “yan kasar nan, musamman matasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Taron Paris, Tinubu Ya Tafi Birnin Landan

Next Post

‘Yan Nijeriya 125 Da Suka Makale A Sudan Za Su Iso Abuja Yau Asabar

Related

Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

2 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
‘Yan Nijeriya 125 Da Suka Makale A Sudan Za Su Iso Abuja Yau Asabar

‘Yan Nijeriya 125 Da Suka Makale A Sudan Za Su Iso Abuja Yau Asabar

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.