ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za A Rage Ricikin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya -Miyetti Allah

by Abubakar Abba
3 years ago
miyetti allah

Shugaban kungiyar Fulani makiyya ta kasa reshen jihar Bauchi Miyetti Allah ta bayyana cewa, dawo da amfani da burtaloli kasar nan ne kawai mafita kan kawo karshen ricikin da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin manoma da makiyyan kasar nan.

Shugaban kungiyar reshen jihar Alhaji Sadikue Ibrahim Ahmed a wata hirarsa da manema labarai a jihar Bauchi, inda shugaban ya yi nuni da cewa, batar da burtaloli kasar nan ne Fulani makiyya komawa cikin jeji.

  • Yadda Aka Yi Fito-na-fito Da Masu Gidaje Da Jami’an Rusau A Kano

Sadikue ya bayyana cewa, hakan ya jano fulanin makiyaya suke yin kaura zuwa jeji a lokacin rani don su samu su ciyar da dabbobin su.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, amma a yau dabbobin na makiyya sun kasance suna yin kiwo a kan tituna wasu kuma suna kwana a cikin kwangaye.

“Hakan ya jano fulanin makiyaya suke yin kaura zuwa jeji a lokacin rani don su samu su ciyar da dabbobin su.”

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ya sanar da cewa, tun kafin zuwan turawa cikin kasar nan, akwai burtaloli da dabbobin makiyan ke bi, inda ya yi nuni da cewa, hatta wasu guaren da aka kebewa makiyyan wasu mutanen sun yi gine-gine akansu
Shugaban kungiyar ya bayana cewa, sai idan gwamnati ta dawo da burtulolin ne kamar yadda ake da su a jamhuriyya ta biyu a kasar nan, sannan za a samu sa’ida kan yawan samu rikece-rikice a tsakanin makiyya da manoma.

“Tun kafin zuwan turawa cikin kasar nan, akwai burtaloli da dabbobin makiyan ke bi, inda ya yi nuni da cewa, hatta wasu guaren da aka kebewa makiyyan wasu mutanen sun yi gine-gine akansu.”

Ya sanar da cewa, irin cin kashin da ake yiwa makiyya a kasar nan abin takaici ne, inda ya kara da cewa, da yawan su an kore su daga guraren da kakaknsu suke tun asali kusan sama da shakaru 100. duk shekara, ana yawan samu rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani makiyya a kasar nan.

A wani labarin kuwa, masana a fannin noman Rogo a kasar nan sun bayyana cewa, daga cikin tan miliyan 53 na Rogon da ake noma wa a Nijeriya a duk shekara, sama da kashi 90 a cikin dari ana sarrafa Rogon zuwa sauran wasu nau’ukan abinci.

A cewarsu, kiididdga ce ta tabbatar da wannan adadin, inda masanan suka kara da cewa, fannin na noman Rogon ya taimaka wajen samar wa da miliyoyin ‘yan Nijeriya aikin yi idan kuma aka inganta fannin, zai samar fiye da hakan.

Masanan sun sanar da hakan ne a a taron kara wa juna sani da suka gudanar a Babban Birnin Tarayyar Abuja, inda kuma suka yi nuni da cewa,kokarin da gwamtin tarayya ke ci gaba da yi na sake farfado noman na Rogo a Nijeriya, musamman kan daukain da Babban Bankin Nijeriya CBN ke samar wa a fannin, inda ya yi nuni da cewa, CBN ya bayar da gagarumar gudunawa wajen bunkasa fannin na noman Rogo a kasar nan.

“Kokarin na gwamtin tarayya ga fannin abin yaba wa ne matuka, musamman ganin cewa, nomansa na daya daga cikin amfanin gona da ke kara karfafa tattalin arzikin duniya”.

A cewar masanan, Nijeriya ce ke a kan gaba wajen noman Rogo, inda suka bayyana cewa, kasar na samar da kimanin tan miliyan 53 na Rogo a shekarar 2018 tare da kuma ta ke samar da akalla tan 7.7 ako wacce kadada daya, idan aka kwatanta da tan 23.4 da kuma tan 22.2 da ake samarwa a kasashen in Indonesiya da Thailand.

Masanan sun sanar cewa, ci gaba da sake farfado noman na Rogo a Nijeriya da gwamnati ke ci gaba da yi, musamman ta hanyar yin amfani da daukin da kan Babban Bankin Nijeriya ya kara taimaka wa matuka wajen kara bunkasa fannin na noman Rogon a kasar, da Kara fitar da shi zuwa kasuwar duniya, inda kuma hakan ya kara samar wa gwamnatin kasar kudaden shiga masu dimbin yawa.

“Nijeriya ce ke a kan gaba wajen noman Rogo, inda suka bayyana cewa, kasar na samar da kimanin tan miliyan 53 na Rogo a shekarar 2018 tare da kuma ta ke samar da akalla tan 7.7 ako wacce kadada daya, idan aka kwatanta da tan 23.4 da kuma tan 22.2 da ake samarwa a kasashen in Indonesiya da Thailand”.

Masanan sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi dukkan mai yuwa wajen kara samar da masu zuba jari a fannin na noman Rogon a kasar, musamman idan aka yi la’akari da irin dimbin kudaden shiga da fannin ke samar wa da manoman Rogon a kasar, inda kuma suka yi yi nuni da cewa, hakan zai kara taimaka wa wajen kara samar da ayyukan yi ga “yan kasar nan, musamman matasa.

miyetti allah
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
‘Yan Nijeriya 125 Da Suka Makale A Sudan Za Su Iso Abuja Yau Asabar

‘Yan Nijeriya 125 Da Suka Makale A Sudan Za Su Iso Abuja Yau Asabar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.