• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago ta Kasa(NLC) da sauran dukkan gwamayyar kungiyoyi da suka gudanar da zanga-zangar lumana ta kwanaki biyu a fadin kasar nan, sun bayyana cewa ba za su sarara ba har sai gwamnatin tarayya ta kawo karshen yajin aikin Kungiyar Malaman Jami’o’in Nijeriya (ASUU).

Sun bayyana cewa manufar wannan zanga-zangar dai ita ce, tilasta wa gwamnatin tarayya ta biya bukatun ASUU, domin a bude jami’o’in gwamnatin taraya ta yadda dalibai za su ci gaba da daukan darasi.

Yadda ’Yan Kasuwa Suka Rufe Kasuwanni A Legas Don Yankar Katin Zabe

Da yake jawabi ga ma’aikata a Abuja, shugaban kungiyar NLC na kasa, Kwamared Ayuba Wabba ya jaddada cewa, kungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai gwamnatin tarayya ta biya dukkan bukatun kungiyar ASUU.

Kwamared Wabba ya bayyana cewa babu wani dalilin da zai sa yaran talakawa za su ci gaba da zama a gidan iyayensu na tsawan watani biyar, yayin da ‘ya’yan masu kudi suke ci gaba da karatu a kasashen ketare.
Ya ce, “Babu adalci a cikin wannan lamari idan har gwamnati ta kasa kawo karshen lamari, ba za mu taba gajiya ba kuma ba za mu yi fushi ba, saboda ba wannan yarjejeniya muka kulla da shugabannin da muka zaba ba.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

“Wannan somin-tabi ne, dole ne ku yi shirin fargfado da bangaren ilimi, mun gaji da halin ko-in-kula na gwamnati, dole ne mu rungumi kaddara a hannunmu.
“Sun ce muna janyo barazanar tsaro, amma abin da su suke yi baraza ce da dimokuradiyya, za mu sake saita kasar nan ta yadda shugabanninmu za su gudanar da abubuwan da suka dace.

“Muna yaba wa gwamnoni wadanda suka fito domin yin jawabi, muna bukatar gudanar da tattauna ta yadda za a kawo karshen lamarin, ba za mu taba yarda mutane kalilan su ruguza goben yaran Nijeriya ba,” in ji shi.
Shi ma da yake gabatar da jawabi, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa dole ne gwamnatin tayya ta kaddamar da tsarin gudanarwa na biyan malaman jami’o’i.

Hakazalika, kungiyar NLC reshan Jihar Legas ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makanni biyu na kawo karshen yajin aikin ASUU ko kuma ta fuskanci zazzafar zanga-zanga.

Shugaban kungiyar NLC reshan Jihar Legas, Kwamared Agnes Funmi Sessi shi ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi a gaban dinbin masu zanga-zanga a ofishin gwamnatin Jihar Legas. Ya nuna takaicinsa ta yadda iyaye da dalibain jami’o’in gwamnatin tarayya suke ciki, inda ya ce shi ne makasudin gudanar da wannan zanga-zanga na gargadi.

A ranar 26 ga watan Yulin 2022, kungiyar NLC ta gudanar da zanga-zangar gargadi na kwanaki biyu a dukkan fadin kasar nan, sakamakon gwamnatin tarayya ta kasa kawo karshen yajin aikin kungiyar ASUU. Kungiyar ta gargadin gwamnatin tarayya kar ta dauki wannan zanga-zanga da wasa, domin idan har ta yi kunnen kashi, to zanga-zangan za ta iya rikidewa fiye da wanda aka samu na EndSARS a shekarar 2020.

Kungiyar ASUU ta tsunduma cikin yajin aiki na tsawan watanni biyar, sakamakon rashin cika mata alkawarin da gwamnatin tarayya ba ta yi ba, wadanda suka hada da alawus din malaman jami’o’i da gyara tsarin jami’o’in Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya (Ra’yinmu)

Next Post

Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita – Hon. Almustapha

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

3 hours ago
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
Labarai

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

5 hours ago
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu
Labarai

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

6 hours ago
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina
Labarai

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

7 hours ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

10 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

11 hours ago
Next Post
Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita – Hon. Almustapha

Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita - Hon. Almustapha

LABARAI MASU NASABA

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.