• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago ta Kasa(NLC) da sauran dukkan gwamayyar kungiyoyi da suka gudanar da zanga-zangar lumana ta kwanaki biyu a fadin kasar nan, sun bayyana cewa ba za su sarara ba har sai gwamnatin tarayya ta kawo karshen yajin aikin Kungiyar Malaman Jami’o’in Nijeriya (ASUU).

Sun bayyana cewa manufar wannan zanga-zangar dai ita ce, tilasta wa gwamnatin tarayya ta biya bukatun ASUU, domin a bude jami’o’in gwamnatin taraya ta yadda dalibai za su ci gaba da daukan darasi.

Yadda ’Yan Kasuwa Suka Rufe Kasuwanni A Legas Don Yankar Katin Zabe

Da yake jawabi ga ma’aikata a Abuja, shugaban kungiyar NLC na kasa, Kwamared Ayuba Wabba ya jaddada cewa, kungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai gwamnatin tarayya ta biya dukkan bukatun kungiyar ASUU.

Kwamared Wabba ya bayyana cewa babu wani dalilin da zai sa yaran talakawa za su ci gaba da zama a gidan iyayensu na tsawan watani biyar, yayin da ‘ya’yan masu kudi suke ci gaba da karatu a kasashen ketare.
Ya ce, “Babu adalci a cikin wannan lamari idan har gwamnati ta kasa kawo karshen lamari, ba za mu taba gajiya ba kuma ba za mu yi fushi ba, saboda ba wannan yarjejeniya muka kulla da shugabannin da muka zaba ba.

Labarai Masu Nasaba

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

“Wannan somin-tabi ne, dole ne ku yi shirin fargfado da bangaren ilimi, mun gaji da halin ko-in-kula na gwamnati, dole ne mu rungumi kaddara a hannunmu.
“Sun ce muna janyo barazanar tsaro, amma abin da su suke yi baraza ce da dimokuradiyya, za mu sake saita kasar nan ta yadda shugabanninmu za su gudanar da abubuwan da suka dace.

“Muna yaba wa gwamnoni wadanda suka fito domin yin jawabi, muna bukatar gudanar da tattauna ta yadda za a kawo karshen lamarin, ba za mu taba yarda mutane kalilan su ruguza goben yaran Nijeriya ba,” in ji shi.
Shi ma da yake gabatar da jawabi, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa dole ne gwamnatin tayya ta kaddamar da tsarin gudanarwa na biyan malaman jami’o’i.

Hakazalika, kungiyar NLC reshan Jihar Legas ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makanni biyu na kawo karshen yajin aikin ASUU ko kuma ta fuskanci zazzafar zanga-zanga.

Shugaban kungiyar NLC reshan Jihar Legas, Kwamared Agnes Funmi Sessi shi ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi a gaban dinbin masu zanga-zanga a ofishin gwamnatin Jihar Legas. Ya nuna takaicinsa ta yadda iyaye da dalibain jami’o’in gwamnatin tarayya suke ciki, inda ya ce shi ne makasudin gudanar da wannan zanga-zanga na gargadi.

A ranar 26 ga watan Yulin 2022, kungiyar NLC ta gudanar da zanga-zangar gargadi na kwanaki biyu a dukkan fadin kasar nan, sakamakon gwamnatin tarayya ta kasa kawo karshen yajin aikin kungiyar ASUU. Kungiyar ta gargadin gwamnatin tarayya kar ta dauki wannan zanga-zanga da wasa, domin idan har ta yi kunnen kashi, to zanga-zangan za ta iya rikidewa fiye da wanda aka samu na EndSARS a shekarar 2020.

Kungiyar ASUU ta tsunduma cikin yajin aiki na tsawan watanni biyar, sakamakon rashin cika mata alkawarin da gwamnatin tarayya ba ta yi ba, wadanda suka hada da alawus din malaman jami’o’i da gyara tsarin jami’o’in Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya (Ra’yinmu)

Next Post

Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita – Hon. Almustapha

Related

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

15 minutes ago
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama
Labarai

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

1 hour ago
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

3 hours ago
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
Labarai

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

4 hours ago
NLC
Labarai

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

5 hours ago
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu
Labarai

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

5 hours ago
Next Post
Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita – Hon. Almustapha

Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita - Hon. Almustapha

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
NLC

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.