ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
NLC

Kungiyar Kwadago ta Kasa(NLC) da sauran dukkan gwamayyar kungiyoyi da suka gudanar da zanga-zangar lumana ta kwanaki biyu a fadin kasar nan, sun bayyana cewa ba za su sarara ba har sai gwamnatin tarayya ta kawo karshen yajin aikin Kungiyar Malaman Jami’o’in Nijeriya (ASUU).

Sun bayyana cewa manufar wannan zanga-zangar dai ita ce, tilasta wa gwamnatin tarayya ta biya bukatun ASUU, domin a bude jami’o’in gwamnatin taraya ta yadda dalibai za su ci gaba da daukan darasi.

Yadda ’Yan Kasuwa Suka Rufe Kasuwanni A Legas Don Yankar Katin Zabe

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi ga ma’aikata a Abuja, shugaban kungiyar NLC na kasa, Kwamared Ayuba Wabba ya jaddada cewa, kungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai gwamnatin tarayya ta biya dukkan bukatun kungiyar ASUU.

Kwamared Wabba ya bayyana cewa babu wani dalilin da zai sa yaran talakawa za su ci gaba da zama a gidan iyayensu na tsawan watani biyar, yayin da ‘ya’yan masu kudi suke ci gaba da karatu a kasashen ketare.
Ya ce, “Babu adalci a cikin wannan lamari idan har gwamnati ta kasa kawo karshen lamari, ba za mu taba gajiya ba kuma ba za mu yi fushi ba, saboda ba wannan yarjejeniya muka kulla da shugabannin da muka zaba ba.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Wannan somin-tabi ne, dole ne ku yi shirin fargfado da bangaren ilimi, mun gaji da halin ko-in-kula na gwamnati, dole ne mu rungumi kaddara a hannunmu.
“Sun ce muna janyo barazanar tsaro, amma abin da su suke yi baraza ce da dimokuradiyya, za mu sake saita kasar nan ta yadda shugabanninmu za su gudanar da abubuwan da suka dace.

“Muna yaba wa gwamnoni wadanda suka fito domin yin jawabi, muna bukatar gudanar da tattauna ta yadda za a kawo karshen lamarin, ba za mu taba yarda mutane kalilan su ruguza goben yaran Nijeriya ba,” in ji shi.
Shi ma da yake gabatar da jawabi, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa dole ne gwamnatin tayya ta kaddamar da tsarin gudanarwa na biyan malaman jami’o’i.

Hakazalika, kungiyar NLC reshan Jihar Legas ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makanni biyu na kawo karshen yajin aikin ASUU ko kuma ta fuskanci zazzafar zanga-zanga.

Shugaban kungiyar NLC reshan Jihar Legas, Kwamared Agnes Funmi Sessi shi ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi a gaban dinbin masu zanga-zanga a ofishin gwamnatin Jihar Legas. Ya nuna takaicinsa ta yadda iyaye da dalibain jami’o’in gwamnatin tarayya suke ciki, inda ya ce shi ne makasudin gudanar da wannan zanga-zanga na gargadi.

A ranar 26 ga watan Yulin 2022, kungiyar NLC ta gudanar da zanga-zangar gargadi na kwanaki biyu a dukkan fadin kasar nan, sakamakon gwamnatin tarayya ta kasa kawo karshen yajin aikin kungiyar ASUU. Kungiyar ta gargadin gwamnatin tarayya kar ta dauki wannan zanga-zanga da wasa, domin idan har ta yi kunnen kashi, to zanga-zangan za ta iya rikidewa fiye da wanda aka samu na EndSARS a shekarar 2020.

Kungiyar ASUU ta tsunduma cikin yajin aiki na tsawan watanni biyar, sakamakon rashin cika mata alkawarin da gwamnatin tarayya ba ta yi ba, wadanda suka hada da alawus din malaman jami’o’i da gyara tsarin jami’o’in Nijeriya.

NLC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita – Hon. Almustapha

Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita - Hon. Almustapha

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.