ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Malamin Jami’a Ya Yi Barazanar Ajiye Aiki Kan Rashin Albashi

by Najib Sani
4 years ago
Dakta Auwal Mustapha Imam

Dakta Auwal Mustapha Imam

Wani malami a  Jami’ar Tarayya da ke Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi, Dakta Auwal Mustapha Imam, ya yi barazanar ajiye aikinsa matukar gwamnati ta ki biyan malamai albashinsu na watanni da suke bi tun bayan tsunduma yajin aikin ASUU.

Ya bayyana hakan ne a hirarsa da LEADERSHIP Hausa, Inda ya ce shi ne kadai malamin da yake da digiri uku a duk tsangayar, inda ya sha alwashin barin aiki a Jami’ar matukar ba a biya shi albashinsa na watannin baya ba.

  • Zan Mayar Da Jami’o’i Karkashin Kulawar Gwamnatocin Jihohi Idan Na Zama Shuagaban Kasa – Atiku
  •  ‘Yan Daba Sun Tarwatsa Taron Gangamin Takarar Atiku A Ribas

A cewarsa, malamai masu yajin aikin sun cancanci a biya su albashinsu na watannin da suke yajin aiki, inda ya yi ikirarin cewa duk da sun rufe azuzuwa amma suna yin bincike na ilimi da kuma duba kundin daliban da ke shirin kammala digiri saboda haka sun cancanci a basu albashi.

ADVERTISEMENT

Ya ayyana matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na kin biyansu albashi don sun tafi yajin aiki a matsayin mugunta.

“An saka mu cikin wahala da gangan, muna cikin talauci. Mutane na cikin bashi da matsaloli iri-iri. Akwai wadanda a cikinmu motar haya suka koma tukawa, wasu sun sayar da motocinsu. Rashin kyautawa ne, zalunci ne gwamnati ta ce ba zata ba da wannan kudin ba” Inji shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Malamin ya ci gaba da cewa akwai ire-irensa da yawa da zasu bar aikin, su nemi wasu wuraren da za a mutunta su muddin aka ki biyansu albashin watannin baya.

Imam ya jaddada cewa sun tafi yajin aikin ne domin kubutar da ilimin jami’oi kada ta lalace kamar yadda gwamnati ta lalata makarantun firamare da sakandare a cewarsa.

Babban malamin, ya ce daya daga cikin abubuwan da suke bukata daga gwamnati shi ne a ba jami’oi damar yin amfani da kudadensu na shiga.

Ya ce jami’oi suna amfani da kudadensu wajen biyan wasu malamai daga wasu wurare saboda karancin malaman jami’a a kasar nan, inda ya yi nuni da cewa muddin ba a ba su ‘yancin cin gashin kansu ba game da kudadensu, to, ba za su iya daukar malaman haya ba don cike gurbin rashin isassun malamai na dindindin a makarantunsu.

ASUU
Najib Sani
+ postsBio
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Kur’ani Bai Halatta Cin Naman Kare Ba-Sheikh Masussuka
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Sin Za Ta Jagoranci Samar Da Kundin Tsarin Amfani Da Sabbin Makamashin Samar Da Lantarki Na Farko A Duniya

Sin Za Ta Jagoranci Samar Da Kundin Tsarin Amfani Da Sabbin Makamashin Samar Da Lantarki Na Farko A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.