ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Malamin Jami’a Ya Yi Barazanar Ajiye Aiki Kan Rashin Albashi

by Najib Sani
4 years ago
Dakta Auwal Mustapha Imam

Dakta Auwal Mustapha Imam

Wani malami a  Jami’ar Tarayya da ke Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi, Dakta Auwal Mustapha Imam, ya yi barazanar ajiye aikinsa matukar gwamnati ta ki biyan malamai albashinsu na watanni da suke bi tun bayan tsunduma yajin aikin ASUU.

Ya bayyana hakan ne a hirarsa da LEADERSHIP Hausa, Inda ya ce shi ne kadai malamin da yake da digiri uku a duk tsangayar, inda ya sha alwashin barin aiki a Jami’ar matukar ba a biya shi albashinsa na watannin baya ba.

  • Zan Mayar Da Jami’o’i Karkashin Kulawar Gwamnatocin Jihohi Idan Na Zama Shuagaban Kasa – Atiku
  •  ‘Yan Daba Sun Tarwatsa Taron Gangamin Takarar Atiku A Ribas

A cewarsa, malamai masu yajin aikin sun cancanci a biya su albashinsu na watannin da suke yajin aiki, inda ya yi ikirarin cewa duk da sun rufe azuzuwa amma suna yin bincike na ilimi da kuma duba kundin daliban da ke shirin kammala digiri saboda haka sun cancanci a basu albashi.

ADVERTISEMENT

Ya ayyana matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na kin biyansu albashi don sun tafi yajin aiki a matsayin mugunta.

“An saka mu cikin wahala da gangan, muna cikin talauci. Mutane na cikin bashi da matsaloli iri-iri. Akwai wadanda a cikinmu motar haya suka koma tukawa, wasu sun sayar da motocinsu. Rashin kyautawa ne, zalunci ne gwamnati ta ce ba zata ba da wannan kudin ba” Inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Malamin ya ci gaba da cewa akwai ire-irensa da yawa da zasu bar aikin, su nemi wasu wuraren da za a mutunta su muddin aka ki biyansu albashin watannin baya.

Imam ya jaddada cewa sun tafi yajin aikin ne domin kubutar da ilimin jami’oi kada ta lalace kamar yadda gwamnati ta lalata makarantun firamare da sakandare a cewarsa.

Babban malamin, ya ce daya daga cikin abubuwan da suke bukata daga gwamnati shi ne a ba jami’oi damar yin amfani da kudadensu na shiga.

Ya ce jami’oi suna amfani da kudadensu wajen biyan wasu malamai daga wasu wurare saboda karancin malaman jami’a a kasar nan, inda ya yi nuni da cewa muddin ba a ba su ‘yancin cin gashin kansu ba game da kudadensu, to, ba za su iya daukar malaman haya ba don cike gurbin rashin isassun malamai na dindindin a makarantunsu.

ASUU
Najib Sani
+ postsBio
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Kur’ani Bai Halatta Cin Naman Kare Ba-Sheikh Masussuka
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Sin Za Ta Jagoranci Samar Da Kundin Tsarin Amfani Da Sabbin Makamashin Samar Da Lantarki Na Farko A Duniya

Sin Za Ta Jagoranci Samar Da Kundin Tsarin Amfani Da Sabbin Makamashin Samar Da Lantarki Na Farko A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.