ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Malamin Jami’a Ya Yi Barazanar Ajiye Aiki Kan Rashin Albashi

by Najib Sani
4 years ago
Dakta Auwal Mustapha Imam

Dakta Auwal Mustapha Imam

Wani malami a  Jami’ar Tarayya da ke Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi, Dakta Auwal Mustapha Imam, ya yi barazanar ajiye aikinsa matukar gwamnati ta ki biyan malamai albashinsu na watanni da suke bi tun bayan tsunduma yajin aikin ASUU.

Ya bayyana hakan ne a hirarsa da LEADERSHIP Hausa, Inda ya ce shi ne kadai malamin da yake da digiri uku a duk tsangayar, inda ya sha alwashin barin aiki a Jami’ar matukar ba a biya shi albashinsa na watannin baya ba.

  • Zan Mayar Da Jami’o’i Karkashin Kulawar Gwamnatocin Jihohi Idan Na Zama Shuagaban Kasa – Atiku
  •  ‘Yan Daba Sun Tarwatsa Taron Gangamin Takarar Atiku A Ribas

A cewarsa, malamai masu yajin aikin sun cancanci a biya su albashinsu na watannin da suke yajin aiki, inda ya yi ikirarin cewa duk da sun rufe azuzuwa amma suna yin bincike na ilimi da kuma duba kundin daliban da ke shirin kammala digiri saboda haka sun cancanci a basu albashi.

ADVERTISEMENT

Ya ayyana matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na kin biyansu albashi don sun tafi yajin aiki a matsayin mugunta.

“An saka mu cikin wahala da gangan, muna cikin talauci. Mutane na cikin bashi da matsaloli iri-iri. Akwai wadanda a cikinmu motar haya suka koma tukawa, wasu sun sayar da motocinsu. Rashin kyautawa ne, zalunci ne gwamnati ta ce ba zata ba da wannan kudin ba” Inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Malamin ya ci gaba da cewa akwai ire-irensa da yawa da zasu bar aikin, su nemi wasu wuraren da za a mutunta su muddin aka ki biyansu albashin watannin baya.

Imam ya jaddada cewa sun tafi yajin aikin ne domin kubutar da ilimin jami’oi kada ta lalace kamar yadda gwamnati ta lalata makarantun firamare da sakandare a cewarsa.

Babban malamin, ya ce daya daga cikin abubuwan da suke bukata daga gwamnati shi ne a ba jami’oi damar yin amfani da kudadensu na shiga.

Ya ce jami’oi suna amfani da kudadensu wajen biyan wasu malamai daga wasu wurare saboda karancin malaman jami’a a kasar nan, inda ya yi nuni da cewa muddin ba a ba su ‘yancin cin gashin kansu ba game da kudadensu, to, ba za su iya daukar malaman haya ba don cike gurbin rashin isassun malamai na dindindin a makarantunsu.

ASUU
Najib Sani
+ postsBio
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Kur’ani Bai Halatta Cin Naman Kare Ba-Sheikh Masussuka
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Sin Za Ta Jagoranci Samar Da Kundin Tsarin Amfani Da Sabbin Makamashin Samar Da Lantarki Na Farko A Duniya

Sin Za Ta Jagoranci Samar Da Kundin Tsarin Amfani Da Sabbin Makamashin Samar Da Lantarki Na Farko A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.