• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Rasha Da Yukrain: Buhari Ya Koka Da Kwararowar Makamai Afirka

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
Buhari

A ranar Talata ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa a halin yanzu makaman da ake amfani da su a yakin da ake tafkawa a tsakanin kasar Rasha da Yukrain sun fara shigowa yakin tafkin tekun Chadi, inda daga na za su bazu zuwa sauran kasashen Afrika, wanda hakan zai cigaba da kara wutar mastalar tsaron da ake fuskanta a yankin.

Ita dai yankin kogin Chadi yana da dinbin albarkan tattalin arziki ya kuma hada yankunan Yammaci da Tsakiyar Afrika da suka hada da kasashen Cameroon, Chadi, Nijar da Nijeriya.

  • 2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli
  • Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Shugabga Buhari ya yi wannan bayanin ne a yayin bude babba taron shugabannin kungiyar kasashen yakin tafkin kogin Chadi a karo na 16 da aka yi a babban dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja, shugaban kasa wanda kuma shi ne shugaban kungiyar, ya ce, yakin na Rasha da Yukrain ya kara haifar da bazuwa kananan makamai a sassan duniya wanda hakan kuma ya karfafa kirar bukatar a kara tabbatar da tsaro a iyakokin kasashen yankin don katse yiwuwar shigowar makamai daga wadannan yankin.

Daga nan shugaban kasa Buhari ya kuma kara bayyana cewa, rikicin kasar Rasha da Yukrain da saura yankunan da ke fuskantar tashe-tashen hankula suka bunkasa harkokin ‘yan ta’addan Boko Haram a yankin Yammacin Afrika.

Ya ce, duk da kokarin da ake yi na rage karfin ‘yan Boko Haram, har yanzu kungiyar na nan na cigaba da ayyukanta na ta’addanci.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

“Ina farin cikin sanar da ku cewa, akan wannan shawarar muka karfafa ayyukan rundunar hadin gwiwa na MNJTF inda suka gudanar da aikinsu cikin nasara ta hanyar gabatar da rukunin aikin fafatawa har sau uku da aka sa wa suna kamar haka ’Ops‘YANCIN TAFKI (I&II) da ‘Ops Lake Sanity I’ da kuma ‘Ops Lake Sanity II’, za kuma a shirya mataki na gaba ne bayan tattara bayanai da darussan da aka cimma a shirye-shiryen mu na baya.

“Ina ma farin cikin sanar da ku cewa a yayin gabatar da farmakin ‘Ops Lake Sanity I’ an samu nasarar kashe mayakan Boko Haram da dama.

“ya za dole mu kwana da sanin cewa, duk wadanna nasarorin da kungiyar MNJTF ta samu a kan ‘yan ta’addan har yanzu akwai barazanar ‘yan ta’adda a wasu yankunanmu.

A nasa jawabin, babban sakataren hukumar LCBC, Ambasada Mamman Nuhu, ya sanar da cewa, Nijeriya ta biya kasonta na Dala 209,075,748 don tafiyar da rundunar hadin gwiwa ta MNJTF daga shekarar 2015 zuwa 2021.

Taron ya samu halartar shugabanni 6 na kasashen kungiyar in banda shugaban kasa Cameron, Paul Biya wanda ya samu wakilcin daya daga cikin ministocinsa.

Shugabannin kasashe da suka samu hakarta sun hada da Farfesa Faustine Archange TOUADERA, na Jamhoriyya Afrika ta Tsakiya; Mohamed BAZOUM, na kasa Nijar; Patrice TALLON, na jamhoriyyar Benin; Mahamat Idriss Deby ITNO, na kasar Chad da Mohamed AL-MENFI, na kasar Libya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Da Dumi-duminsa: 'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

LABARAI MASU NASABA

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.