• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Rasha Da Yukrain: Buhari Ya Koka Da Kwararowar Makamai Afirka

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Yakin Rasha Da Yukrain: Buhari Ya Koka Da Kwararowar Makamai Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa a halin yanzu makaman da ake amfani da su a yakin da ake tafkawa a tsakanin kasar Rasha da Yukrain sun fara shigowa yakin tafkin tekun Chadi, inda daga na za su bazu zuwa sauran kasashen Afrika, wanda hakan zai cigaba da kara wutar mastalar tsaron da ake fuskanta a yankin.

Ita dai yankin kogin Chadi yana da dinbin albarkan tattalin arziki ya kuma hada yankunan Yammaci da Tsakiyar Afrika da suka hada da kasashen Cameroon, Chadi, Nijar da Nijeriya.

  • 2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli
  • Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Shugabga Buhari ya yi wannan bayanin ne a yayin bude babba taron shugabannin kungiyar kasashen yakin tafkin kogin Chadi a karo na 16 da aka yi a babban dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja, shugaban kasa wanda kuma shi ne shugaban kungiyar, ya ce, yakin na Rasha da Yukrain ya kara haifar da bazuwa kananan makamai a sassan duniya wanda hakan kuma ya karfafa kirar bukatar a kara tabbatar da tsaro a iyakokin kasashen yankin don katse yiwuwar shigowar makamai daga wadannan yankin.

Daga nan shugaban kasa Buhari ya kuma kara bayyana cewa, rikicin kasar Rasha da Yukrain da saura yankunan da ke fuskantar tashe-tashen hankula suka bunkasa harkokin ‘yan ta’addan Boko Haram a yankin Yammacin Afrika.

Ya ce, duk da kokarin da ake yi na rage karfin ‘yan Boko Haram, har yanzu kungiyar na nan na cigaba da ayyukanta na ta’addanci.

Labarai Masu Nasaba

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

“Ina farin cikin sanar da ku cewa, akan wannan shawarar muka karfafa ayyukan rundunar hadin gwiwa na MNJTF inda suka gudanar da aikinsu cikin nasara ta hanyar gabatar da rukunin aikin fafatawa har sau uku da aka sa wa suna kamar haka ’Ops‘YANCIN TAFKI (I&II) da ‘Ops Lake Sanity I’ da kuma ‘Ops Lake Sanity II’, za kuma a shirya mataki na gaba ne bayan tattara bayanai da darussan da aka cimma a shirye-shiryen mu na baya.

“Ina ma farin cikin sanar da ku cewa a yayin gabatar da farmakin ‘Ops Lake Sanity I’ an samu nasarar kashe mayakan Boko Haram da dama.

“ya za dole mu kwana da sanin cewa, duk wadanna nasarorin da kungiyar MNJTF ta samu a kan ‘yan ta’addan har yanzu akwai barazanar ‘yan ta’adda a wasu yankunanmu.

A nasa jawabin, babban sakataren hukumar LCBC, Ambasada Mamman Nuhu, ya sanar da cewa, Nijeriya ta biya kasonta na Dala 209,075,748 don tafiyar da rundunar hadin gwiwa ta MNJTF daga shekarar 2015 zuwa 2021.

Taron ya samu halartar shugabanni 6 na kasashen kungiyar in banda shugaban kasa Cameron, Paul Biya wanda ya samu wakilcin daya daga cikin ministocinsa.

Shugabannin kasashe da suka samu hakarta sun hada da Farfesa Faustine Archange TOUADERA, na Jamhoriyya Afrika ta Tsakiya; Mohamed BAZOUM, na kasa Nijar; Patrice TALLON, na jamhoriyyar Benin; Mahamat Idriss Deby ITNO, na kasar Chad da Mohamed AL-MENFI, na kasar Libya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariRashaUkraineYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shiga Firgici: ’Yan Bindiga Sun Cinna Wa Fadar Iree Wuta A Osun

Next Post

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Related

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

7 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

8 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

9 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

12 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

1 day ago
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Da Dumi-duminsa: 'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.