• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakubu Maikyau Ya Zama Sabon Shugaban Lauyoyi (NBA) Na Kasa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Yakubu Maikyau Ya Zama Sabon Shugaban Lauyoyi (NBA) Na Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Lauya mai mukamin (SAN), Mista Yakubu Chonoko Maikyau, ya samu nasarar zama sabon shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa (NBA).

Maikyau ya samu nasarar ne a zaben da NBA ta gudanar da karfe 12 na safiya zuwa zuwa karfe 11.59 na daren ranar Asabar.

  • CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023
  • Tarayyar Turai Za Ta Yi Nazari Kan Lafta Wa Rasha Karin Takunkumai

Ya samu nasarar ne bayan samun kuri’u 22,342 da hakan ya kai shi ga kada ‘yan takara biyu wato Messrs Joe-Kyari Gadzama (SAN), shugaban kwamitin tsaro na NBA da kuma tsohon sakataren Janar na NBA, Jonathan Taidi.

Kamar yadda shugaban kwamitin zaben NBA, Ayodele Akintunde (SAN), ya sanar a taron manema labarai ya ce masu zabe 59,392 ne suka yi rajistar zaben yayin da kuma sama da masu zaben 3,000 suka gaza samun dama bisa gaza tantancesu.

Ya kara da cewa, mutum 34,809 ne suka kada kuri’ar kwatankwacin kaso 58.61 na adadin wadanda suka dace su yi zaben.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

Ya ce Maikyau ya samu kuri’u 22,342 kwatankwacin kaso 64.6 cikin dari na wadanda suka kada kuri’ar da hakan ya ba shi damar shiga ofishin Shugaban NBA na kasa.

Ya kuma ce, Gadzama SAN ya samu kuri’u 10,842 yayin da kuma Taidi ya samu kuri’u 1,380 kacal.

Kazalika wakilinmu ya nakalto cewa, Adesina Adegbite ya zama sakataren Janar na NBA yayin da kuma Daniel Ka-Ayli ya zama mataimakin sakataren janar.

Chinyere Obasi kuma aka zaba a matsayin Sakataren walwala da jin dadin mambobin NBA na kasa, sai kuma Habeeb Lawal ya zama sakataren watsa labarai, Olawole Ajiboye ya zama mataimakin sakataren watsa labarai sai kuma Anze-Bishop Ladidi ya zama mai rike da lalitar NBA wato ma’aji.

Kungiyar lauyoyin ta kuma zabi Linda Bala a matsayin mataimakin shugabar kungiyar na 1 da kuma zabin Clement Ugo mataimakin shugaban na 2 da Amanda Demechi-Asagba mataimakin shugaban NBA na 3.

Kazalika NBA ta zabi Lauyoyi 20 a matsayin mambobin majalisar kolinta da da su wakilci shiyyoyin Yammaci, Gabashi da Arewaci a fadin kasar nan.

Da ya ke jawabin amsar ragamar mulkin NBA, Barista Yakubu SAN ya nemi hadin kan dukkanin mambobin kungiyar da su dafa masa domin Kai kungiyar zuwa ha tudun mun-tsira.

Ya ce zai tabbatar da walwalwarsu da jin dadinsu gami kuma da kare musu kima da mutunci a kowani lokaci domin saukaka musu yanayin aiki a fadin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MaikyauNBASabon ShugabaSANZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023

Next Post

Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

Related

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

2 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

12 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

13 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

17 hours ago
Next Post
Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.