ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakubu Maikyau Ya Zama Sabon Shugaban Lauyoyi (NBA) Na Kasa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Maikyau

Babban Lauya mai mukamin (SAN), Mista Yakubu Chonoko Maikyau, ya samu nasarar zama sabon shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa (NBA).

Maikyau ya samu nasarar ne a zaben da NBA ta gudanar da karfe 12 na safiya zuwa zuwa karfe 11.59 na daren ranar Asabar.

  • CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023
  • Tarayyar Turai Za Ta Yi Nazari Kan Lafta Wa Rasha Karin Takunkumai

Ya samu nasarar ne bayan samun kuri’u 22,342 da hakan ya kai shi ga kada ‘yan takara biyu wato Messrs Joe-Kyari Gadzama (SAN), shugaban kwamitin tsaro na NBA da kuma tsohon sakataren Janar na NBA, Jonathan Taidi.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban kwamitin zaben NBA, Ayodele Akintunde (SAN), ya sanar a taron manema labarai ya ce masu zabe 59,392 ne suka yi rajistar zaben yayin da kuma sama da masu zaben 3,000 suka gaza samun dama bisa gaza tantancesu.

Ya kara da cewa, mutum 34,809 ne suka kada kuri’ar kwatankwacin kaso 58.61 na adadin wadanda suka dace su yi zaben.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya ce Maikyau ya samu kuri’u 22,342 kwatankwacin kaso 64.6 cikin dari na wadanda suka kada kuri’ar da hakan ya ba shi damar shiga ofishin Shugaban NBA na kasa.

Ya kuma ce, Gadzama SAN ya samu kuri’u 10,842 yayin da kuma Taidi ya samu kuri’u 1,380 kacal.

Kazalika wakilinmu ya nakalto cewa, Adesina Adegbite ya zama sakataren Janar na NBA yayin da kuma Daniel Ka-Ayli ya zama mataimakin sakataren janar.

Chinyere Obasi kuma aka zaba a matsayin Sakataren walwala da jin dadin mambobin NBA na kasa, sai kuma Habeeb Lawal ya zama sakataren watsa labarai, Olawole Ajiboye ya zama mataimakin sakataren watsa labarai sai kuma Anze-Bishop Ladidi ya zama mai rike da lalitar NBA wato ma’aji.

Kungiyar lauyoyin ta kuma zabi Linda Bala a matsayin mataimakin shugabar kungiyar na 1 da kuma zabin Clement Ugo mataimakin shugaban na 2 da Amanda Demechi-Asagba mataimakin shugaban NBA na 3.

Kazalika NBA ta zabi Lauyoyi 20 a matsayin mambobin majalisar kolinta da da su wakilci shiyyoyin Yammaci, Gabashi da Arewaci a fadin kasar nan.

Da ya ke jawabin amsar ragamar mulkin NBA, Barista Yakubu SAN ya nemi hadin kan dukkanin mambobin kungiyar da su dafa masa domin Kai kungiyar zuwa ha tudun mun-tsira.

Ya ce zai tabbatar da walwalwarsu da jin dadinsu gami kuma da kare musu kima da mutunci a kowani lokaci domin saukaka musu yanayin aiki a fadin kasar nan.

Maikyau
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.