ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakubu Maikyau Ya Zama Sabon Shugaban Lauyoyi (NBA) Na Kasa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Maikyau

Babban Lauya mai mukamin (SAN), Mista Yakubu Chonoko Maikyau, ya samu nasarar zama sabon shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa (NBA).

Maikyau ya samu nasarar ne a zaben da NBA ta gudanar da karfe 12 na safiya zuwa zuwa karfe 11.59 na daren ranar Asabar.

  • CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023
  • Tarayyar Turai Za Ta Yi Nazari Kan Lafta Wa Rasha Karin Takunkumai

Ya samu nasarar ne bayan samun kuri’u 22,342 da hakan ya kai shi ga kada ‘yan takara biyu wato Messrs Joe-Kyari Gadzama (SAN), shugaban kwamitin tsaro na NBA da kuma tsohon sakataren Janar na NBA, Jonathan Taidi.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban kwamitin zaben NBA, Ayodele Akintunde (SAN), ya sanar a taron manema labarai ya ce masu zabe 59,392 ne suka yi rajistar zaben yayin da kuma sama da masu zaben 3,000 suka gaza samun dama bisa gaza tantancesu.

Ya kara da cewa, mutum 34,809 ne suka kada kuri’ar kwatankwacin kaso 58.61 na adadin wadanda suka dace su yi zaben.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya ce Maikyau ya samu kuri’u 22,342 kwatankwacin kaso 64.6 cikin dari na wadanda suka kada kuri’ar da hakan ya ba shi damar shiga ofishin Shugaban NBA na kasa.

Ya kuma ce, Gadzama SAN ya samu kuri’u 10,842 yayin da kuma Taidi ya samu kuri’u 1,380 kacal.

Kazalika wakilinmu ya nakalto cewa, Adesina Adegbite ya zama sakataren Janar na NBA yayin da kuma Daniel Ka-Ayli ya zama mataimakin sakataren janar.

Chinyere Obasi kuma aka zaba a matsayin Sakataren walwala da jin dadin mambobin NBA na kasa, sai kuma Habeeb Lawal ya zama sakataren watsa labarai, Olawole Ajiboye ya zama mataimakin sakataren watsa labarai sai kuma Anze-Bishop Ladidi ya zama mai rike da lalitar NBA wato ma’aji.

Kungiyar lauyoyin ta kuma zabi Linda Bala a matsayin mataimakin shugabar kungiyar na 1 da kuma zabin Clement Ugo mataimakin shugaban na 2 da Amanda Demechi-Asagba mataimakin shugaban NBA na 3.

Kazalika NBA ta zabi Lauyoyi 20 a matsayin mambobin majalisar kolinta da da su wakilci shiyyoyin Yammaci, Gabashi da Arewaci a fadin kasar nan.

Da ya ke jawabin amsar ragamar mulkin NBA, Barista Yakubu SAN ya nemi hadin kan dukkanin mambobin kungiyar da su dafa masa domin Kai kungiyar zuwa ha tudun mun-tsira.

Ya ce zai tabbatar da walwalwarsu da jin dadinsu gami kuma da kare musu kima da mutunci a kowani lokaci domin saukaka musu yanayin aiki a fadin kasar nan.

Maikyau
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.