ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakubu Maikyau Ya Zama Sabon Shugaban Lauyoyi (NBA) Na Kasa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Maikyau

Babban Lauya mai mukamin (SAN), Mista Yakubu Chonoko Maikyau, ya samu nasarar zama sabon shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa (NBA).

Maikyau ya samu nasarar ne a zaben da NBA ta gudanar da karfe 12 na safiya zuwa zuwa karfe 11.59 na daren ranar Asabar.

  • CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023
  • Tarayyar Turai Za Ta Yi Nazari Kan Lafta Wa Rasha Karin Takunkumai

Ya samu nasarar ne bayan samun kuri’u 22,342 da hakan ya kai shi ga kada ‘yan takara biyu wato Messrs Joe-Kyari Gadzama (SAN), shugaban kwamitin tsaro na NBA da kuma tsohon sakataren Janar na NBA, Jonathan Taidi.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban kwamitin zaben NBA, Ayodele Akintunde (SAN), ya sanar a taron manema labarai ya ce masu zabe 59,392 ne suka yi rajistar zaben yayin da kuma sama da masu zaben 3,000 suka gaza samun dama bisa gaza tantancesu.

Ya kara da cewa, mutum 34,809 ne suka kada kuri’ar kwatankwacin kaso 58.61 na adadin wadanda suka dace su yi zaben.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ya ce Maikyau ya samu kuri’u 22,342 kwatankwacin kaso 64.6 cikin dari na wadanda suka kada kuri’ar da hakan ya ba shi damar shiga ofishin Shugaban NBA na kasa.

Ya kuma ce, Gadzama SAN ya samu kuri’u 10,842 yayin da kuma Taidi ya samu kuri’u 1,380 kacal.

Kazalika wakilinmu ya nakalto cewa, Adesina Adegbite ya zama sakataren Janar na NBA yayin da kuma Daniel Ka-Ayli ya zama mataimakin sakataren janar.

Chinyere Obasi kuma aka zaba a matsayin Sakataren walwala da jin dadin mambobin NBA na kasa, sai kuma Habeeb Lawal ya zama sakataren watsa labarai, Olawole Ajiboye ya zama mataimakin sakataren watsa labarai sai kuma Anze-Bishop Ladidi ya zama mai rike da lalitar NBA wato ma’aji.

Kungiyar lauyoyin ta kuma zabi Linda Bala a matsayin mataimakin shugabar kungiyar na 1 da kuma zabin Clement Ugo mataimakin shugaban na 2 da Amanda Demechi-Asagba mataimakin shugaban NBA na 3.

Kazalika NBA ta zabi Lauyoyi 20 a matsayin mambobin majalisar kolinta da da su wakilci shiyyoyin Yammaci, Gabashi da Arewaci a fadin kasar nan.

Da ya ke jawabin amsar ragamar mulkin NBA, Barista Yakubu SAN ya nemi hadin kan dukkanin mambobin kungiyar da su dafa masa domin Kai kungiyar zuwa ha tudun mun-tsira.

Ya ce zai tabbatar da walwalwarsu da jin dadinsu gami kuma da kare musu kima da mutunci a kowani lokaci domin saukaka musu yanayin aiki a fadin kasar nan.

Maikyau
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Next Post
Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

Jarumar Nollywood, Ada Ameh Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.