• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ku Zo Mu Yi Aiki Tare A Katsina – Mai Ba Gwamna Shawara

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Siyasa
0
‘Yan Adawa Ku Zo Mu Yi Aiki Tare A Katsina – Mai Ba Gwamna Shawara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai ba gwamnan jihar Katsina shawara kan harkokin siyasa, Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo, ya yi kira ga ‘yan adawa da su zo a yi gwamnati domin ci gaban al’ummar jihar Katsina baki ɗaya.

Hon. Ya’u Gwajo-Gwajo ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai jin kaɗan bayan shigarsa sabon ofis na mai baiwa gwamna shawara kan harkokin siyasa.

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin ya ce, in dai da gaske adawa ake yi, to yana kira da babbar murya da su zo a haɗa kai a ciyar da jihar gaba domin duk abinda ake yi ana yi ne domin talaka.

Hon. Gwajo-Gwajo ya ce a shirye suke da sauraren suka mai ma’ana, domin a cewarsa suka ba laifi ba ne, idan har zata sa abyi gyara wanda zai amfani al’umma baƙi ɗaya.

“Muna son ɗan adawa ya zo ya faɗi abinda yake ganin ba daidai bane, muna san haka, domin shi duk wanda ya ce gyara kayanka ai baya zama sauke mu raba” Cewarsai.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

A cewar Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo abinda ba daidai ba shi ne, a kawo abu da babu shi, amma don gwamnati ta ce zata yi wani abu ɗan adawa ya ce ba daidai bane, za a tsaya a duba wannan abu a gani domin samun maslaha.

‘Yan adawa muna maraba da ku, muna gayyatar ku, ku zo a yi wannan gwamnati da ku, domin ta haka ne jihar Katsina zata kai wani matsayi da ba a tunani’ inji Gwajo-Gwajo.

Haka kuma ya yi kira ga ‘yan jarida da su bada ta su gudunmawa wajan ganin wannan gwamnati ta Malam Dikko Raɗɗa ta yi nasara, inda ya ce ‘yan jarida suna muhimmiyar rawar da za su taka wajan kawo gyara a tsarin dimokuraɗiyya.

Ya yi kira ga ‘Yan jarida da su ci gaba da aikinsu ta hanyar tuntuɓar gwamnati akan abinda ya shafe ta kai tsaye, inda ya yi alkawarin cewa kofa a buɗe take akan duk wani ƙarin haske daga ɓangaren gwamnati.

Kazalika ya bada tabbacin cewa wannan ofis ɗin shi, a shirye yake wajan ganin ya yi aiki da kowane ɓangare tunda ofis ne na siyasa, a cewarsa ofis ɗin yana da alaƙa da kowane ɓangare na gwamnatin jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Next Post

Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

Related

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

1 day ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

2 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

2 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

3 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

4 days ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

6 days ago
Next Post
Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

LABARAI MASU NASABA

gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.