• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ku Zo Mu Yi Aiki Tare A Katsina – Mai Ba Gwamna Shawara

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Siyasa
0
‘Yan Adawa Ku Zo Mu Yi Aiki Tare A Katsina – Mai Ba Gwamna Shawara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai ba gwamnan jihar Katsina shawara kan harkokin siyasa, Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo, ya yi kira ga ‘yan adawa da su zo a yi gwamnati domin ci gaban al’ummar jihar Katsina baki ɗaya.

Hon. Ya’u Gwajo-Gwajo ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai jin kaɗan bayan shigarsa sabon ofis na mai baiwa gwamna shawara kan harkokin siyasa.

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin ya ce, in dai da gaske adawa ake yi, to yana kira da babbar murya da su zo a haɗa kai a ciyar da jihar gaba domin duk abinda ake yi ana yi ne domin talaka.

Hon. Gwajo-Gwajo ya ce a shirye suke da sauraren suka mai ma’ana, domin a cewarsa suka ba laifi ba ne, idan har zata sa abyi gyara wanda zai amfani al’umma baƙi ɗaya.

“Muna son ɗan adawa ya zo ya faɗi abinda yake ganin ba daidai bane, muna san haka, domin shi duk wanda ya ce gyara kayanka ai baya zama sauke mu raba” Cewarsai.

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

A cewar Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo abinda ba daidai ba shi ne, a kawo abu da babu shi, amma don gwamnati ta ce zata yi wani abu ɗan adawa ya ce ba daidai bane, za a tsaya a duba wannan abu a gani domin samun maslaha.

‘Yan adawa muna maraba da ku, muna gayyatar ku, ku zo a yi wannan gwamnati da ku, domin ta haka ne jihar Katsina zata kai wani matsayi da ba a tunani’ inji Gwajo-Gwajo.

Haka kuma ya yi kira ga ‘yan jarida da su bada ta su gudunmawa wajan ganin wannan gwamnati ta Malam Dikko Raɗɗa ta yi nasara, inda ya ce ‘yan jarida suna muhimmiyar rawar da za su taka wajan kawo gyara a tsarin dimokuraɗiyya.

Ya yi kira ga ‘Yan jarida da su ci gaba da aikinsu ta hanyar tuntuɓar gwamnati akan abinda ya shafe ta kai tsaye, inda ya yi alkawarin cewa kofa a buɗe take akan duk wani ƙarin haske daga ɓangaren gwamnati.

Kazalika ya bada tabbacin cewa wannan ofis ɗin shi, a shirye yake wajan ganin ya yi aiki da kowane ɓangare tunda ofis ne na siyasa, a cewarsa ofis ɗin yana da alaƙa da kowane ɓangare na gwamnatin jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Next Post

Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

23 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

1 day ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

1 day ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

5 days ago
Next Post
Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.