• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Adawa Sun Mayar Da Martani Game Da Cika Shekara Daya Na Mulkin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
jam'iyyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan adawa sun siffanta mulkin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu na tsawon shekara daya a matsayin bai tsinana wa ‘yan Nijeriya da komi ba.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya bayyana cewa shekarar farko na mulkin Tinubu bai haifar da da mai ido ba, saboda bai aiwatar da wani tsari na a zo a gani ba.
Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitara a ranar Talata.

  • Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu 
  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara

A cewarsa, lokacin da aka rantsar da Tinubu ya lasa wa ‘yan Nijeriya zuma a baki na cewa zai farfado da tattalin arziki da samar da ayyukan yi da samar da tsaro da kawo karshen fatara a kasar nan.

Atiku ya ce lokacin da ‘yan Nijeriya suka ji kalamansa sai suka dauka zai kawo musu sauki a kan ukubar da suka sha na mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na tsawon shekara 8.

“Tinubu bai yi wani tsari kan sake farfado da tattalin arziki ba, sai dai ma ya kara dagula lamura.
“A watan Mayun 2023, ya cire tallafin man fetur, bayan wata daya kuma, babban bankin Nijeriya ya kaddamar da sabon tsari kan hada-hadar canjin kudaden waje na bai daya.

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

“Wadannan tsari sun yi matukar raunata tattalin arzikin kasar nan, wanda suka kara talauta ‘yan Nijeriya tun daga wannan lokaci har zuwa yau.”

A nasa bangaren, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore, ya siffanta shekara daya na mulkin Tinubu a matsayin gazawa ta karshe.

Sowore idan shi malami ne zai rushe ajin da Tinubu yake da ya ba shi maki. Dan takarar shugaban kasan na AAC ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita.

“Idan ni malami ne ba zan taba bai wa Tinubu maki kan mulkinsa na shekara guda ba, ni zan ma rutse ajin ne saboda babu abin da za a iya ba shi na maki.

“Ina mai tabbatar da cewa wannan mulki na shekara guda ba mu karu da komi ba. An samu hauhawar farashin kayayyaki wanda ba a taba samu ba, rashin ayyukan yi ya kara kazanta, rashin tsaro ya kara ta’azzara a cikin shekara daya, sannan kuma gwamnati ta kasa biyan mafi karancin albashi.”

Su kuwa ‘yan majalisa na jam’iyyar LP sun bayyana cewa Tinubu bai cika alkawarin da ya yi wa ‘yan Nijeriya lokacin yakin neman zabe a tsawon mulkinsa na shekara daya ba.

Sun ce an samu karuwar rashin tsaro da matsin tattailin arziki a tsawon mulkin Tinubu na shekara guda.
‘Yan majalisar karkashin jagorancin Afam Ogene ya ce ‘yan Nijeriya za a tambaya ko Tinubu ya cika alkawarin da ya yi a cikin shekara guda.

Sun dai yi Kiara da Shugaba Tinubu da ya gaggauta rage wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da suke fama da shi a halin yanzu, tare da tabbatar an samu wadataccen abinci da ruwan sha da kiwon lafiya da kuma ingantaccen ilimi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCJam'iyyun SiyasaNNPPPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Nijeriya Ga ‘Yan Majalisa: Yunwa Ta Fi Damun Mu Ba Sauya Taken Kasa Ba

Next Post

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

40 minutes ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

2 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

6 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

6 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

8 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

9 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.