ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Nijeriya Ga ‘Yan Majalisa: Yunwa Ta Fi Damun Mu Ba Sauya Taken Kasa Ba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Majalisar Dattawa

‘Yan Nijeriya sun nuna damuwarsu kan yadda Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya maida hankali wajen sanya hannu kan dokar canza taken Nijeriya zuwa ga koma wa amfani da tsohon na da baya maimakon duba wahalhalun da suke sha.

A ranar Laraba ne dai, Shugaban Tinubu ya tattaba hannu kan dokar komawa amfani da tsohon taken Nijeriya, lamarin ya biyo bayan gabatar da kudurin da amincewa da shi da ‘yan majalisun wakilai da na dattawa suka yi ne a makon jiya.

  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki CBN Kan Korar Ma’aikata 600
  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara

Sai dai kuma kafin sanya hannu kan dokar, Babban Antoni kuma ministan shari’a (AGF) Lateef Fagbemi, SAN, ya bukaci ‘yan majalisun dokokin kasa da ka da su amince da kudurin doka da ke neman a koma amfani da tsohon taken Nijeriya a maimakon wanda ake amfani da shi a halin yanzu.

ADVERTISEMENT

Fabgemi ya kuma yi gargadin cewa ka da ‘yan majalisun su yi riga malam masallaci wajen canza taken kasar nan, amma duk da wannan kiran nasa ‘yan majalisu sun ci gaba da aikinsu har ta kai ga shugaban kasa ya sanya hannu, inda yanzu kudurin ya zama doka.

Ministan wanda ya nuna adawarsa kan sauya taken a wajen taron jin ba’asi kan kudurin wanda kwamitin majalisar dattawa kan shari’a, kare hakkin Bil’adama da harkokin shari’a ta shirya a ranar Litinin a Abuja, Fabgemi ya yi gargadin cewa ka da ‘yan majalisa su yi amfani da karfin majalisa wajen amincewa da kudurin ba tare da bai wa ‘yan kasa damar tofa albarkacin bakinsu ba.

LABARAI MASU NASABA

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Ya lura bisa kan cewa bai kamata a je ga kokarin gyara dokar da za ta kai ga canza taken kasa zuwa tsohon na da a kan wanda ake tafiya a tare da shi a halin yanzu ba tare da shigo da kowa da kowa cikin lamarin ba.

“A wasu lokutan taken kasa na fito ne daga irin gasa daga wajen ‘yan kasa. Misali za a iya baje taken kasar da ake da shawara a kai a tafka muhawa kafin a kai ga amincewa ko ayyanawa.

“Babban abun nufi a nan shi ne, a samar da taken da ke da ra’ayin jama’a da goyon bayansu domin tabbatar da cewa taken ta tafi daidai da muradinsu, zamantakewa da kuma siyasar wannan zamanin.
“Don haka ina adawa da ra’ayin kawai a ce tunanin canza taken kasa zai fito ne daga wajen ‘yan majalisa ko shugaban kasa kawai.

“Maimakon hakan a ji yo ra’ayoyin jama’an kasa kan tunanin canza taken kasa, walau a koma amfani da na da baya ko kuma a kirkiro sabo, don haka akwai bukatar a gudanar da jin ba’asin jama’a a shiyyoyi tare da tattaro shawarwarin shugabannin tarayya, jihohi, ‘yan majalisun tarayya da na Jihohi, da sauransu.

“Ta hakan ne za a samu nasarar fito da hakikanin abun da masu rinjaye na kasar ke da bukata.”
Shi ma da yake gargadin ‘yan majalisun kasa, wani fitaccen lauya, Cif Mike Ozekhome (SAN), ya yi kira da a tattaro shawarori da ra’ayoyin ‘yan kasa daga lungu da sako kafin a yi maganar canza taken na kasa.
A cewarsa, ta hakan ne ra’ayoyin ‘yan kasa gabaki daya zai gamsu kuma za a samu nasarar fito da abun da za su yi na’am da shi.

Sai dai dan majalisar wakilai, Mohammed Shehu Fagge, ya yi suka ne kan matakin da aka dauka na dawo da tsohon taken, inda ya yi tsokaci cewa, kawo wannan magana na sauya taken rashin sanin ciwon kai ne.
Shehu, ya ce a wannan hali da ‘yan kasa ke ciki na yunwa, fatara da rashi da sauran abubuwa makamantansu su ya fi dacewa a mayar da hankali a kai.

Ya ce shugabanin majalisa ba su yi tunani ba, domin ba shi ne abin da ‘yan kasa ke so ba.
Ya ce kamata ya yi a kalli dokoki da za su amfana wa talakan kasa da abubuwa da za su kawo wa rayuwarsu sauyi.

Shehu ya ce har yanzu majalisa ba ta kammala aiki kan kasafin kudin 2024 ba, saboda haka yana kira da a fuskanci bukatun al’umma.

Shi ma wani dan Nijeriya mazaunin Jihar Bauchi, Ibrahim Muhammad, ya shan mamakin wannan matakin, “Ban san mene ne asalin dalilin da ke boye wajen canza taken kasar nan cikin kankanin lokaci ba, tun daga gabatar da kudirin zuwa amincewa da shi na fara tunani a kan kudirin. Gaskiya a halin da muke ciki na yunwa da fatara kar a dame mu da batun komawa tson taken kasa, a yi mana abun da ya dace ba.

“Ya kamata ko su ‘yan majalisu ba su yi zurfin tunani ba, ina dauka shugaban kasa zai yi abun da ya dace amma kash, gaskiya ba mu tsammaci hakan ba, dubban ‘yan kasa zai yi wuya su iya haddace wannan taken da aka koma, abun kunya ne ‘yan kasa su kasa iya karanto takensu, da yunwa za mu ji ko da wani haddace sabon taken da aka canza,” ya shaida.

Majalisa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
Labarai

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
Labarai

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Next Post
jam'iyyu

’Yan Adawa Sun Mayar Da Martani Game Da Cika Shekara Daya Na Mulkin Tinubu

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.