ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Adawa Sun Mayar Da Martani Game Da Cika Shekara Daya Na Mulkin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
jam'iyyu

‘Yan adawa sun siffanta mulkin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu na tsawon shekara daya a matsayin bai tsinana wa ‘yan Nijeriya da komi ba.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya bayyana cewa shekarar farko na mulkin Tinubu bai haifar da da mai ido ba, saboda bai aiwatar da wani tsari na a zo a gani ba.
Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitara a ranar Talata.

  • Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu 
  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara

A cewarsa, lokacin da aka rantsar da Tinubu ya lasa wa ‘yan Nijeriya zuma a baki na cewa zai farfado da tattalin arziki da samar da ayyukan yi da samar da tsaro da kawo karshen fatara a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Atiku ya ce lokacin da ‘yan Nijeriya suka ji kalamansa sai suka dauka zai kawo musu sauki a kan ukubar da suka sha na mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na tsawon shekara 8.

“Tinubu bai yi wani tsari kan sake farfado da tattalin arziki ba, sai dai ma ya kara dagula lamura.
“A watan Mayun 2023, ya cire tallafin man fetur, bayan wata daya kuma, babban bankin Nijeriya ya kaddamar da sabon tsari kan hada-hadar canjin kudaden waje na bai daya.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

“Wadannan tsari sun yi matukar raunata tattalin arzikin kasar nan, wanda suka kara talauta ‘yan Nijeriya tun daga wannan lokaci har zuwa yau.”

A nasa bangaren, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore, ya siffanta shekara daya na mulkin Tinubu a matsayin gazawa ta karshe.

Sowore idan shi malami ne zai rushe ajin da Tinubu yake da ya ba shi maki. Dan takarar shugaban kasan na AAC ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita.

“Idan ni malami ne ba zan taba bai wa Tinubu maki kan mulkinsa na shekara guda ba, ni zan ma rutse ajin ne saboda babu abin da za a iya ba shi na maki.

“Ina mai tabbatar da cewa wannan mulki na shekara guda ba mu karu da komi ba. An samu hauhawar farashin kayayyaki wanda ba a taba samu ba, rashin ayyukan yi ya kara kazanta, rashin tsaro ya kara ta’azzara a cikin shekara daya, sannan kuma gwamnati ta kasa biyan mafi karancin albashi.”

Su kuwa ‘yan majalisa na jam’iyyar LP sun bayyana cewa Tinubu bai cika alkawarin da ya yi wa ‘yan Nijeriya lokacin yakin neman zabe a tsawon mulkinsa na shekara daya ba.

Sun ce an samu karuwar rashin tsaro da matsin tattailin arziki a tsawon mulkin Tinubu na shekara guda.
‘Yan majalisar karkashin jagorancin Afam Ogene ya ce ‘yan Nijeriya za a tambaya ko Tinubu ya cika alkawarin da ya yi a cikin shekara guda.

Sun dai yi Kiara da Shugaba Tinubu da ya gaggauta rage wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da suke fama da shi a halin yanzu, tare da tabbatar an samu wadataccen abinci da ruwan sha da kiwon lafiya da kuma ingantaccen ilimi.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Kwankwaso
Labarai

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane
Manyan Labarai

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Next Post
Manzon Allah

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

June 9, 2026
Kwankwaso

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

June 9, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

June 9, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

June 9, 2026
Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.