• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC A Kaduna Na Kokawa Kan Mayar Da Su Saniyar-ware Wajen Rabon Muƙamai

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kafanchan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoto da BBC ta yi kan wata ɓaraka da ta kunno kai a jihar Kaduna tsakanin wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar dangane da rabon muƙamai a matakin gwamnatin tarayya da na Jiha.

Wasu magoya bayan jam’iyyar a yankunan karkara na zargin cewa ana nuna musu bambanci wajen rabon mukamai, duk kuwa da irin gudunmuwar da suka ce sun bayar a lokacin zaɓe.

  • Gwamnan Uba Sani Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori, Ya Nemi Su Yi Aiki Tukuru
  • PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

Mutanen sun kafa hujja da wasu manyan muƙamai huɗu da suka ce an ba wa wata ƙaramar hukuma guda.

Alhaji Yusuf Owner Dutsen Wai, na ɗaya daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar APCn da ke zargin cewa ba a yi musu adalci ba wajen rabon, ya kuma shaida cewa su mutanen karkara ba a yin komai da su.

Ya ce, ‘‘Mun tura mota ne ta bar mu da hayaƙi saboda dukkan muƙaman nan da aka bayar babu wani ɗan karkara ko guda.”

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

‘‘ Tun daga kan muƙamin minista har zuwa sauran muƙamai an raba wa waɗanda ba su iya cin akwatunan zaɓensu ba, idan har gaskiya ake so idan mutum ɗan jam’iyya ne ai sai a ɗauki muƙami a ba shi ba a dunƙule abu wuri ɗaya kamar ƙwallo ba,” in ji shi.

Shi kuwa Honorabul Umar Sale Koch, daga yankin Kujama na jihar ta Kaduna, shaida wa BBC ya yi cewa, idan har jam’iyyar APCn ba ta ɗauki mataki na waiwayar yankunan karkara wajen rabon muƙaman ba, to hakan ka iya zama barazana ga jam’iyyar tasu a nan gaba.

Ya ce,“ Siyasa aba ce ta jama’a kuma har aka ci gaba da kasancewa a wannan yanayi to zai iya zama barazana ga jam’iyyarmu ta APC, domin yawan ƙuri’u da jama’ar ake samu daga karkara za su ƙaurace wa jam’iyyar.”

Dan siyasar ya ce,“ Idan aka kalli siyasar ma a yanzu gaba ɗayan waɗanda suka fito daga wata jam’iyyar suka yake mu yanzu sun dawo kuma su ne suke ta wawushe muƙaman, mu muna tsaye mun zama ‘yan kallo.”

To sai dai a nata ɓangaren jam’iyyar APC a jihar ta Kaduna ta ce kamata ya yi masu irin wannan ƙorafi su kwantar da hankalinsu kasancewar gwamnatin APCn a matakin tarayya da kuma jiha ta ƙuduri aniyar tafiya tare da kowa.

Honorabul Salisu Tanko Sono, wanda shi ne kakakin jam’iyyar APC a Kaduna, ya ce, ya kamata mutane su rinƙa haƙuri domin ita gwamnati tana da faɗi, kuma mukaman nan yanzu aka fara, mutanen da suke ganin ba a yi da su, su yi haƙuri ana sane da su.

Taƙaddama tsakanin ‘yan siyasa a Nijeriya ba sabon abu ba ne, inda a wasu lokutan har takan kai a samu rarrabuwar kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKadunaUba Sani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Girgizar Kasa Ta Kashe Mutane 2,445 A Afganistan

Next Post

An Horar Da ‘Ya’Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana’o’in Hannu A Jihar Sokoto

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

1 day ago
Next Post
An Horar Da ‘Ya’Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana’o’in Hannu A Jihar Sokoto

An Horar Da 'Ya'Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana'o'in Hannu A Jihar Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.